18/08/2026
Allah yayiwa Annabi Alaihissalam baiwa iri iri, daga cikinta akwai faranta ran duk wanda ya ganShi Alaihissalam, shi ya sa da abu zai sami mutum mara daɗi ya ganShi Alaihissalam sai yaji babu wannan damuwar, ganinSa ya buce ta Sallallahu Alaihi Wasallam.
17/08/2026
Gwargwadon yadda kake ganin girman Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama, gwargwadon yadda Allah Subhanahu Wata’ala yake ganin girmanka.
17/08/2026
Mai ishirniya yana yiwa Annabi Alaihissalam kirari da cewa: Allah ya tsarkake Sa (baShi da aibu ko ɗaya) tun haihuwarSa har ya kai shekara 40, sannan kuma ya baShi Annabta bayan ya kai shekara 40.
17/08/2026
Allah ya baiwa Annabi Alaihissalam damar yin babbar kyauta da kuma ƙaramarta, shi ya sa idan yana so ba sai yayi tunani ba ko kuma ya jira wahayi, idan yaso kawai sai ya faɗi sunan sahabi yace ɗan aljannah ne, ko kuma idan an roƙe shi aljannah kawai sai yace na baka, wannan itace babbar kyauta.
Ƙaramar kyauta kuma itace wacce zai baiwa mutum raƙumi ɗari, ya sake ƙara masa ɗari, ya sake ƙara masa ɗari, ko ya baiwa mutum ɗanyan zinare akwati guda wanda bazai iya ɗauka ba, duk wata kyauta da ake yinta amfaninta na duniya ne itace ƙaramar kyauta.
17/08/2026
Duk abinda kake so awajen Allah, kasa Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam a gaba, ko menene abinda kake buƙata, saboda girman Manzon Allah Alaihissalam, Allah zai maka ita.
16/08/2026
Annabi Alaihissalam daga kanSa zance ya ƙare, duk wani abu da zaka faɗa, kana faɗar nasa ka gama ƙurewa.
16/08/2026
Akwai wani bature sunansa Michael H. Hart, ya wallafa littafi mai suna The 100: A ranking of the most influntial persons in history, a ranar ƙaddamar da littafin sai hayaniya a hall din gabatarwar, saboda ya saka Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam a lamba ɗaya, suna fara hayaniya yace dasu suyi shiru, Annabi Alaihissalam ya fara kira izuwa musulunci, sai mace guda ɗaya ta yarda (Nana Kadija), sannan namiji ɗaya (Sayyiduna Abubakar), sai wani namijin guda ɗaya wanda bai kai ɗayan shekaru ba (Sayyiduna Ali), yau a duniya akwai musulmai sama da biliyan ɗaya da rabi, shin kuna ganin mutum ɗaya zai yaudari sama da mutum biliyan ɗaya da rabi? sannan kuma ga addinin da ya zo dashi, sama da shekara 1000 bai canza ba, daga nan ne yayi musu wata tambaya: Idan aka faɗi kalma ɗaya mara kyau akanSa (Annabi Alaihissalam) wannan mutum biliyan ɗayan da rabi, dukkansu ko kuma rabinsu za su bayar da rayuwar su, shin a kirista akwai mutum ɗaya da idan aka taɓa Annabi Isa Alaihissalam zai yarda ya bada ransa?!!!
Zance ya ƙare anan kowa yayi shiru aka barshi ya cigaba da bayanin littafinsa, shi ya sa nake masa kirari da Annabin Annabawa kuma Annabi mai yawan albarka.
16/08/2026
Kaf Alam babu wanda aka tantance komai na sa da tausiƙi (tabbas) akan aikinsa ko maganarsa sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam.