Al-Mansur Yahya Muh'd Bargi

Al-Mansur Yahya Muh'd Bargi

Share

بسم الله الرحمن الرحيم

Manufarmu ita ce farfaɗo da tunani, a kan asasin ilimi da hankali

21/05/2026

GADIR KHUM: Ranar da aka kammala Addinin Musulunci (na 1/14)

Bayan kammala Hajjin Bankwana wato (Hajjatul Wada'), na Manzon Allah (SAW) sai ya jagoranci ayarin Musulmi wajen komawa Madina. Yana tare da mutane sama da dubu ɗari (100,000+) a tare da shi – kuma wannan shi ne mafi yawan taron Musulmi da ya taɓa jagoranta.

A lokacin da s**a isa wani wuri da ake kira Ghadir Khum– wani tafki kusa da mahaɗar hanyoyi huɗu wato (Madina, Misira, Iraƙi, Sham da Najdu) – sai aka saukar da umurnin Allah ga Annabi (SAW) wato.

Ayar Tabligh (isar da saƙo) (Al-Ma'ida: 67) ta zo:

Ya Manzon Allah! Ka isar da bayanin da aka saukar gare ka daga Ubangijinka,idan kuwa ba ka aikata ba, to fa k**ar ba ka isar da saƙon annabtar taka ba ne kwata-kwata! Idan kana tsro ne to Allah zai kare ka daga sharrin mutanen, Allah ba ya shiryar da kafirai masu ƙin aikata umarnin Allah!
Wannan ayar tana daga ayoyi masu zafi ba aya ce irin ta yau da kullum ba. Allah yana cewa: idan baka isar da wannan saƙo ba, to dukkan saƙonka bai isa ba!!! Wannan ya nuna cewa abin da zai faɗa yana da matuƙar muhimmanci – yana daidai da dukkan risalar Annabcinsa (sawa).

Nan take sai Annabi (SAW) ya umurci ayarin: na gaba su tsaya, na baya su hanzarto. Ya sa aka share wuri, aka haɗa kayan raƙuma ya zama mumbari. Sai ya hau, ya kalli taron, bayan ya yi godiya da Allah ya yi huɗuba sai kuma ya ɗaga hannun Imam Ali (AS) har mutane na hango fararen hammatansa, sannan ya faɗa musu cwa: Man kuntu mawlahu, fa hadha Aliyyun mawlahu.
Duk wanda na kasance shugabansa, to wannan Ali ne shugabansa ne.

Bayan haka ya ƙara da addu'ar cewa:

Allahumma waali man waalahu, wa aadi man aadaahu, wa anṣur man naṣarahu, wa akh dhul man khadhalahu, wa adir al-ḥaqqa ma'ahu ḥaythu dara.
Wato: Ya Allah, Ka taimake wanda ya taimake shi, Ka tozarta wanda ya tozarta shi, Ka sanya gaskiya ta bi shi duk inda ya juya.

Wannan ba ƙaramar magana ce ba. Kuma ba ƙaramin saƙo ne ba, wanda Annabi ya isar zuwa ga al'umma gaba ɗaya.

TO SHIN:

1. Idan har Allah Ya ce wa Annabi (sawa) "Idan baka isar da wannan saƙon ba, to k**ar baka isar da komai ba" shin me yake nufi game da muhimmancin wannan saƙon?

2. Shin akwai wani sahabi da Annabi (SAW) ya taɓa tsayar da dukan ayarin musulmi irin wannan, ya ɗaga hannunsa, ya ce wa mutane "Wannan shi ne shugabanku a cikin tarihin musulunci"?

3. Mene ne ra'ayinku a kan kalmar "mawla" shin tana nufin aboki ne kawai ko shugaba mai cikakken iko bayan manzon Allah (sawa)?

Ku biyo ni domin jin
Dalilin saukar Ayar Tabligh dalla-dalla da ra'ayoyin malaman Ahlus Sunna game da ita.
Ku biyo ni don ku ga hujjoji masu ƙarfi daga Alqur'ani, Sahihain, da littattafan malaman Sunni, inshaAllah.



Naku Mansur Yahya Bargi

18/05/2026

Duk wanda bai yadda zai iya yin kuskure ba, to ba zai gane kuskurensa ba, b***e ya ɗauki matakin gyarawa!!!

Mafi yawa idan ka ga saɓani to ka bincika wani ya yi kutse ne a cikin haƙƙi ko matsayin da ba nashi ba!!!

Ko kun lura: duk sanda wani ya zagi wani to darajar mai zagin sai ta fara zubewa a idon masu hankali kafin ta wanda aka zaga.

Barkanmu da ranar masoya ta Duniya.

Darussa daga zaman aure a tsakanin Sayyidi Ali da Sayyida Fatima (A.S)

Imam Ali (AS) yana bayyana halayenta da irin zamantakewarsu, yana cewa:

فَوَاللّه ِ لا اَغْضَبَتْنى وَلا عَصَتْ لى اَمْرا. وَلَقَدْ كُنْتُ اَنْظُرُ اِلَيْها فَتَنْكَشِفُ عَنِّى الْهُمُومُ وَ الأَحْزانُ

Wallahi, ba ta taɓa ɓata mini rai ba, kuma ba ta taɓa saɓa mini a kan wani al’amari ba. Haƙiƙa na kasance idan na kalle ta, damuwa da baƙin ciki su kan gushe daga zuciyata.

📚 كشف الغمة، ج ١، ص ٣۶٣

A tarihin Musulunci, auren Sayyida da Imam Ali a.s wani babban abin koyi ga masoya da ma'aurata ta fuskoki da dama:

Sauƙaƙawa cikin al'amarin auren.

Girmama juna da haƙuri da juna a tsakanin masoya da ma'aurata da irin halin rayuwa da aka tsinci kai a ciki.

Taimakon juna da tausayi a cikin ibada da rayuwa.

Tarbiyyar yara da ɓoye sirrin cikin gida.

06/05/2026
22/12/2025

Ilimi da Tarbiyya a Musulunci (1)

Assalamu alaikum warahmatullahi

Gabatarwa

Wannan shi ne yanki na farko da za mu tattauna a kan ilimi a Musulunci. Mu na son za mu tattauna ne game da nau’o’in ilimi daban-daban da kuma ƙarfin tunani, a mahangar Musulunci bisa karantarwar Imam Ali bn Abu Talib (A.S). kuma, za mu yi magana a kan manufar ilimi ta fuskar zamantakewa da kuma mutum ɗaya, da kuma muhimmancin neman ilimin da kuma tarbiyya a Musulunci. Haka nan, za mu tattauna ma’anar yadda ake horarwa da koyon ilimin. A ƙarshe, za mu yi magana game da (Ijtihadi) da muhimmancinsa a Musulunci bisa mahangar Alƙur’ani da Hadisan Ahlul bayt a.s.

A cikin wannan maudu’i, muna son yin amfani da wasu muhimman littattafai da dama, k**ar haka:

Alƙur’ani Mai girma.
Littafin “The Muqaddimah” (1377), wanda Ibn Khaldun (1332–1406) ya rubuta.
Littafin “Ihya Ulum al-Din” (1105), wanda Imam Abu Hamid al-Ghazali (1058–1111) ya rubuta.
Littafin “Tafsir al-Mizan” (1974), wanda Allamah Sayyid Muhammad Husayn Tabataba’i (1903–1981) ya rubuta.
Littafin “Education and Training” (2003), wanda Shahidi Allamah Morteza Mottahari (1920–1979) ya rubuta.
Littafin “Nahj al-Balagha” (an tattara shi a 1010), wanda Sharif al-Radi (970–1015) ya tattara.
Littafin “Principles of Jurisprudence (Usul al-Fiqh)” (1965), wanda Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr (1935–1980) ya rubuta.

Ilimi yana da alaƙa da gina ɗan’adam ne kai tsaye. Ana samun mahanga ne da tunani da yake da tsayayyun manufofi, ƙa’idoji masu cikakken tsari, da kuma abin da ake kira tsarin doka, tattalin arziki da siyasa, ta hanyar ilimi. Wato ita makarantar ilimi ko tunani wata matattara ce da take son aiwatar da wasu manufofin ɗabi’a, tattalin arziki da siyasa tarbiyya ga mutane, ko dai a matakin mutum ɗaya ko na al’umma baki ɗaya. Wannan kansa wani muhimmin batu ne da dole ne a tattauna shi a nan.

Idan wata manufa ta kasance ta zamantakewa ce, ana ganin cewa dole ne a aiwatar da waɗannan tsare-tsare zuwa ga mutane. -ta hanyar makaranta domin ilmantarwa da tarbiyyantarwa, Dole ne a ilimantar da mutane tare da horar da su ta yadda za su iya aiwatar da waɗancan tsare-tsaren a cikin al’umma, ta hanyar ilimi da tarbiyya. Idan kuma manufar ta shafi mutum ɗaya ne tilo, [to a fili yake cewa ilimantarwa da tarbiyyantar da mutum ɗaya ma abu ne mai muhimmanci.] A Musulunci, ana kiyaye matsayin mutum ɗaya da kuma na al’umma gaba ɗaya. Wato, mutum ba ya rasa [matsayinsa na kai] gaba ɗaya.

Saboda haka, a ƙarshe, akwai wani tsari ko shiri na gina mutum. Ko dai ana gina mutum ne domin aiwatar da tsare-tsaren da aka tsara wa al’umma ko jama’a (kuma shima wannan tsari ko shiri ana ɗaukarsa a matsayin gabatarwa (introduction) ne zuwa ga gina al’umma), ko kuma ana gina mutum ne daidai da manufar gina mutum ɗaya, to lallai wannan dole ne ya zama mataki na farko ko wata hanya ta gina al’umma, kuma shi ne babban buri da hadafi na hankali.

A nan ne ya wajaba mu san muhimmanci da ƙa’idojin tarbiyya da ilimi a Musulunci.

Da farko, shin Musulunci yana ba da muhimmanci ga batun neman ilimi da ilmantarwa? Wato koyo da bayar da ilimi da wayar da kai, ko kuwa a’a?

Wannan tambayar malamai (‘ulama’) sun tattauna ta tun farkon zamani. Wani muhimmin batu kuma shi ne cewa Musulunci addini ne da ke kiran mutane zuwa ga neman ilimi, kuma siffofin wannan ilimin da Musulunci ke ƙarfafa a nema suma an tattauna su ta hannun manyan malamai irin su Ghazali-1, Fayd [Kashani]-2 da sauransu, ta fuskar tarbiyya da ilimi; inda ƙa’idojin ɗabi’a na Musulunci s**a zama mafi girman ƙa’idojin tarbiyya ga ɗan’adam.

Shin wanne irin mutum ne abin koyi ga al’ummah wanda Musulunci yake son ya gina?

Tabbas akwai batutuwa a nan masu muhimmanci da za mu tattauna a kansu, da dukkansu suna da alaƙa da hanyar aiwatar da wani tsari a cikin al’ummah ta hanyar ilimi da tarbiyya.

Sannan shin wacce hanya ce za a bi mafi dacewa wajen horar da mutum wanda zai kasance mai amfanarwa a cikin Al’ummah?

Wata tambayar kuma ita ce, zuwa wanne matsayi ne ilimin tunani ko sanin halayyar mutum (psychology) yake da muhimmanci a cikin koyarwar Musulunci? Misali, a tarbiyya da ilimantar da yara, ko tarbiyyantar da mutum ɗaya ko wata al’umma zuwa ga wani hadafi, wane irin umarni aka tanada, kuma har wane matsayi ne waɗannan umarnin suke da ma’ana ta Zahiri data haƙiƙa a musulunci, kuma har wane matsayi ne ake la’akari da yanayin tunanin wanda za’a tarbiyyantar ? Shin tsoho da sabon tsarin tarbiyya da iliminmu ya dace da koyarwar Musulunci ko a’a?

Za mu ci gaba.......... Insha Allah.

Da fatan za ku ci gaba da kasancewa tare da shafukanmu. Naku, Mansur Yahya Bargi. Mon,22 Dec,2025

https://chat.whatsapp.com/H7ric0Nh8Om0cyLdlkChPN

https://www.facebook.com/AlKadhimiyaFoundation?mibextid=ZbWKwL

10/12/2025

Nana Fatimah Al-Zahra (A.S) Ƴar Ma’aikin Allah (1)

Bismillahir-Rahmanir-Rahim.

A duk lokacin da muke son karanta tarihin wani mutum, karatu na ilimi, wanda zai ka sance a ma’aunin ilimi da hankali, to bincikenmu zai fara ne da tambayar shin wannan mutumin da muke son mu karanta tarihinsa waɗanne abubuwa ne ya samar a cikin rayuwarsa?

Shin wacce gudunmawa ya baiwa duniyar ɗan-adam da har muke son mu karanta tarihinsa, domin mu ɗauki darasi a cikin rayuwarsa? mu amfanar da kanmu da kuma al’ummar da mu ke rayuwa a cikin ta.

Ba bu wani abu da zai yi saura daga tarihin mutum bayan mutuwarsa fiye da abin da ya samarwa ɗan-adam mai amfani ko akasin hakan, ta fuskar duniya ko lahira ko duka biyun.

Sannan daga abubuwan da mutum ya samarwa ɗan-adam ne za muyi amfani wajen sani da kuma fahimtar mutumin, tunaninsa a kan al'amura, da matsayinsa.

Kamar yadda son bincikenmu zai ƙaru da shauƙi da zurfafawa sosai idan ya zama mutumin da muke son yin binciken dangane da shi, wani mutum ne na musamman wato wani mutum ne na Allah, mai matsayi da girma a wurin Allha, mutum ne da ya kasance Allah ya ƙarfafe shi ya goyi bayan ayyukan da ya yi da matsayar da ya ɗauka a cikin rayuwarsa, wato yana da shaida daga Allah na kuɓuta daga dukkan wani nau’i na saɓo, wato shi tsarkakke ne a bisa shaidar Allah, to dukkan wata matsayarsa a kan al’amuran da ya fuskanta a rayuwarsa za su kasance ababen darasi da ko yi a cikin rayuwarmu gwargwadon halinmu.

Hakan ne ya sa Allah S a cikin Alƙur’ani Mai girma ya bayar da labarai (ƙasas) na wasu daga cikin Annabawa da manzanninsa ma su girma, sannan ya yi bayani akan yadda s**a rayu, da irin matsayar da s**a ɗauka a cikin al’amura daban-daban da s**a fuskanta acikin rayuwarsu, a wasu lokutan ƙalubalen da s**a fuskanta a karan kansu, ko da iyalansu, ko makusantansu, ko a tsakaninsu da al’ummomin da su ka zo domin su shiryatar dasu, me yasa Allah ya yi hakan ɗaya daga cikin hikimar hakan shine domin su kasance ababen koyi ga Mutane masu hankali da lura.

Mu haɗu a fita ta gaba..........In sha Allahu

10-12-2025

✍🏻 Mansur Yahya Bargi

https://www.facebook.com/share/1BW8zhJrt7/

08/12/2025

Mu San Aƙidunmu — Tambaya da Amsa (2)

Tambaya

A wasu lokutan wasu nau’oin tambayoyi kan bijiro a zuciyar mutum irin su: shin ta yaya zan iya sanin haƙiƙanin waye Allah, shin shi ne ya halicci kansa? Shin waye ya halicci Allah? ko menene asalin zatinsa mai tsarki? To shin ya halatta mutum ya zurfafa tunani a kan irin waɗannan tambayoyin? Me yasa?

Amsa:

An zo da hani a cikin addini game da zurfafa tunani a kan sanin asalin Zatin Allah, sai dai a cikin ayoyinsa, siffofinsa, da halittunsa.

Hujjojin da malamai a Sunna da Shi’a s**a dogara dasu sune k**ar haka:

A ƙarƙashin tafsirin faɗin Allah {وَأَنَّ إِلَى رَبِّكَ الْمُنْتَهَى} (النجم/42) malamai irin su: Tafsirin Tabari (Suuna) da Tafsirin Majma’ al-Bayan na al-Tabarsi (shi’a) da al-Mizān na al-Tabataba’i (Shi’a)
Malaman sun tafi a kan cewa: duk tunani ko binciken da ya ke ƙoƙarin haurawa zuwa ga sanin haƙiƙanin zatin Allah to wajibi ne ka tsayar da shi, domin hankalin ɗan-adam ba zai iya gane hakikarsa ba.

Kamar yadda malamai irin su: Fakhr al-Razi, at-Tafsīr al-Kabir (Sunna) da Sharif al-Murtadha (shi’a) da Sheikh al-Ṣaduƙ, al-Tawḥid (Shi’a) a ƙarƙashin ayar: {لَيْسَ كَمِثْلِهِ شَيْءٌ} (Shura: 11)
Sun tafi a kan cewa: tunda Allah baya k**a da kowanne irin abu a zatinsa. To hankalin mutum ba zai iya hakaito haƙiƙaninsa ba, domin hankali na iya hango abin da ya ke da kwatankwacinsa ne a ƙwaƙwalwa, Saboda haka sanin ainihin zatin Allah ba zai iya yiwu ba.

Kamar yadda Al-Ƙurṭubi (Sunna) da Al-Tabataba’i (al-Mizan) (shi’a) a ƙarƙashin faɗin Allah {وَلَا يُحِيطُونَ بِهِ عِلْمًا} (Taha: 110)

Saboda babu wani ilimi da zai iya faifaye sanin zatin Allah ,to sanin zatinSa ba zai yiwu ba.

Malamai daga Ahlussuna suna cewa:
Imam Malik: Da aka tambaye shi shin ta yaya Allah ya yi daidata a kan al’arshinsa (istiwa)?” sai ya ce: “Ma’anar daidaitonSa a kan al’arshi ta tabbata, amma yadda take ba mu sani ba, tambaya a kai kuma bidi’a ce.”

Tsokaci:

abu na farko idan Idan Imam Malik yana nufin daidaiton daya tabbata a nan shine daidaito na gangangar jiki to ya saɓa da a binda Shi’a s**a tafi a kansa da kuma abinda nassosi s**a tabbatar cewa Allah ba jiki bane da har zai daidaita a kan wani abu, idan kuma da ma’anar a kan rububiyya ne da tafiyar da duniya to ya yi daidai da abinda Shi’a s**a tafi akai, abu na biyu idan tambaya ta kasance a kan zatin Allah ne to shine za a iya kiransa da bidi’a amma idan mai tambaya yana tambaya ne a kan ayyukan Allah da siffofinsa to ba zai fita daga abin nema ba, amma bidi’antar da tambayar ba zai nisa da kasancewar tambayar daga kaso na farko ba.

Mu haɗu a fita ta gaba..........In sha Allahu
8-12-2025

✍🏼Mansur Yahya Muh'd Bargi.

13/07/2025

Bincike da Nazari a kan Hadisin Ummu Haram (2)

2-Ibn Hajar al-Asƙalani:
A cewarsa: (Fath al-Bari, juzu’i na 6, shafi na 51)
"قيل: كانت خالة النبي من الرضاع... والنبي معصوم فلا يخشى عليه فتنة."
An ce: Ummu Ḥaram ta kasance “Ƙanwar mahaifiyarsa ta hanyar shayarwa” saboda haka ana kallon ta a matsayin muharamarsa ce.
Kuma Manzon Allah (S) shi mutum ne mai tsarki daga aikata zunubi da kuskure (ma’asumi), saboda haka ba a jin tsoron cewa zai faɗa cikin wani abu na fitina ko keta haddi.
Wannan maganar ta Ibn Ḥajar tana ƙoƙarin kare ma’anar hadisin Ummu Haram ne ta hanyoyi biyu:
Ta hanyar nasaba: ya ce wai ance: Ummu Haram tana cikin dangin Annabi (S) ta hanyar shayarwa (wato ƙanwar mahaifiyarsa ta nono), don haka ana kallon su a matsayin muharramai.
Ta hanyar tsarkin Annabta: wato ko da ba ta kasance muharramarsa ba, tun da Manzon Allah (S) tsarkakke ne daga duk wani laifi, ko wata sha’awar da ba ta dace ba, to ba za a ji tsoron wani abu zai ya faru tsakaninsu ba.
Ishkalolinmu dangane da wannan maganar ta Ibn Hajar sune:
1-Kalmar “قِيل” tana nuni ne da ra’ayi mai rauni da rashin tabbaci a tarihi da naƙalto magana. wannan yana nuna cewa hujjar cewa Ummu Ḥaram “muharramarsa ce ta nono” ba hujja ce karɓaɓɓiya ba, domin ba a kawo sunan wadda ta shayar da su ba, ko wani bayani dalla-dalla dake tabbatar da hakan.
2- kasancewarta muharramarsa (S) ba hujja ba ce wajen cire masa ƙwarkwata da yin barci a wajenta hakan ba ya halatta a samu cikakkiyar taɓawa ta jiki da jiki, k**ar cire ƙwarkwata a irin matsayin Annabi (S). -Domin tarbiyyarsa ta girmi halascin shari’a kawai-yana kaucewa duk wani abu da ka iya kawo zargi, ko da an yarda da shi a shari’a. Hausawa ma na cewa ana barin halas ko don kunya.
3-ta ya ya za’ayi amfani da tsarkin Annabi wajen kafa hujja da halasta hulɗar da ba ta dace da matsayinsa ba.
Kyawawan halayensa hujja ne a kan tsarkinsa (S), don haka dole a tabbatar da cewa halin yana daidai da matsayinsa na Annabi da irin tarbiyyar da Allah ya bashi. Wannan yana nufin: duk wata ruwayar da ke nuni da wata mu’amala da ba ta dace da matsayinsa da tsarkinsa ba to wajibi ne ayi raddinta a jefar da ita, ko da isnadinta yana da karfi.
4- Ma’anar wannan hadisin na iya jawo raini da zargi ga martabar Annabi (S) Hadisin yana iya zama kofa ga masu raini ko masu yaɗa ƙyamar Annabi (S) da raunata darajar Annabi a zukatan wasu koda sun kasance musulmai, Hakan kuma ya sabawa manufar Alƙur’ani da ke cewa:
لِتُؤْمِنُوا بِاللَّهِ وَ رَسُولِهِ وَ تُعَزِّرُوهُ وَ تُوَقِّرُوهُ وَ تُسَبِّحُوهُ بُكْرَةً وَ أَصِيلًا الفتح: 9

Lallai Mun aiko da Manzon ne don ku yarda da maganarsa, ku yi imani da Allah, kuma ku taimaki addininSa, sannan ku girmama Shi, ku riƙa yi masa tasbihi safiya da maraice. (al-Fatḥ: 9)
5- Manzon Allah da martabarsa (S) su ya fi cancanta da a girmama fiye da girmama isnadin ruwaya kawai, Ibn Ḥajar ya fi dogaro da usulul-isnad (ƙa'idar karɓar riwaya ta hanyar sahihiyar silsila), a kan dogaro da ingancin abinda ruwayar take ƙunshe da shi, dole ne a haɗa tsakanin isnadi da matan (ma’anar ruwaya), kuma idan matan ya saɓawa tsarkin Annabi wanda yake tabbatacce ne a Alƙur’ani to zai fi dacewa a ƙi karɓar hadisin, ko da isnadinsa sahihi ne. Wannan kuma yana nufin cewa tsarkin Annabi da martabarsa (S) bai k**ata a wajen auna su a taƙaitu da ƙa’idar ilimin rijal kaɗai ba, tabbas matsayin Manzon Allah (S) ya girmi hakan.
..............
Mansur Yahya Bargi 13-7-2025

13/07/2025

Bincike da Nazari a kan Hadisin Ummu Haram (1)
Bismillahir Rahmanir Rahim.
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah, Maɗaukaki, Mai tsarki daga dukkan rauni da kuskure, Wanda Ya aiko Annabin rahama, Muhammad (S), haske mai yalwa, shiriya, da rahama ga talikai. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan gidansa tsarkaka, shi ne wanda Allah Ya girmama da wahayi, Ya tsarkake shi daga dukkan ɗabi’u abin zargi, Ya ɗaukake shi da yi masa tarbiya da kan shi, kuma ya kira shi da cewa:
وَإِنَّكَ لَعَلى خُلُقٍ عَظِيمٍ
Kuma tabbas kai kana kan kyawawan ɗabi’u mafi girma
Wannan ayar ita ce ma’auni na asali wajen nazari, karɓa ko jefar da duk wani abu da ya danganci ɗabi’u ko aiki na wannan Annabin (S). Domin wannan Manzon ba mutum ne kawai ba k**ar kowa; shi rahama ne ga duniya, tsarki ne mai rai, mafifici ne a halayya da aƙida, wanda Allah Ya tabbatar da cewa yana da kunya yana da tarbiyya fiye da kowa.
Ɗaya daga cikin batutuwan da s**a ja hankalin masana hadisi da malaman tarihi shine hadisin Ummu Ḥarām bint Milḥān, wadda aka rawaito cewa Manzon Allah (S) ya ziyarci gidanta kuma tana cire masa ƙwarkwata daga kansa. Wannan riwayar na daga cikin riwayoyin da s**a shahara a cikin littafan Sahihul-Bukhari da Sahihu-Muslim, amma kuma ya fuskanci tirjiya da rashin karɓar shi daga malamai a cikin Sunni da Shi’a saboda yanayin da hadisin ke nunawa dangane da saukar da matsayi, tsarki, tarbiyya, da kunyar Annabi (S).
Nasshin Hadisin da Asalin Sa
Hadisin yana cikin:
Sahih Muslim – Kitabul-Imarah – Babin Faḍhlul-Ghazwi a Bahr: Hadisi: 1912
عن أنس بن مالك، أن رسول الله صلى الله عليه وسلم كان يدخل على أم حرام بنت ملحان، فتطعمه، وكانت تحت عبادة بن الصامت، فدخل عليها رسول الله صلى الله عليه وسلم، فأطعمته، ثم جلست تفلي رأسه، ثم نام، ثم استيقظ وهو يضحك، فقلت: ما يضحكك يا رسول الله؟ قال: ناس من أمتي عرضوا عليّ يركبون هذا البحر كالملوك على الأسرة
Anasu ɗan Malik ya ruwaito cewa:
“Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -da ahlinsa-) ya kasance yana zuwa gidan Ummu Ḥarām ‘yar Milhan, tana masa hidima, tana ba shi abinci. Ita kuma tana auren ‘Ubadah ɗan Samit.
Wata rana Manzon Allah (S) ya shigo wajenta, ta ba shi abinci, sannan ta zauna tana cire masa ƙwarkwata daga kansa (wato ‘ta na 'tafli’).
Bayan haka sai ya yi barci, ya farka yana dariya. Sai na tambaye shi: ‘Ya Manzon Allah, me ya sa kake dariya?’
Sai ya ce: ‘Mutane daga cikin al’ummata sun bayyana a gabana, suna hawa teku k**ar sarakuna a kan gadonsu’”
Me Hadisin ke Nunawa?
Manzon Allah (S) yana zuwa gidan Ummu Haram.
Ita kuwa tana cire masa ƙwarkwata daga kansa (wannan shi ake kira تفلي).
Ya yi barci a gidanta, sannan ya farka yana dariya.
Wannan labarin ya tayar da muhawara mai zafi a tsakanin malamai, domin tabbas irin wannan mu'amala ba ta dace da hali, da matsayi, da tsarkin Annabi (S) ba. Domin labarin yana ɗauke da tambayoyi k**ar haka:
Shin da gaske Annabin tsarki (S) zai iya zaunawa da ƙwarƙwata a jikinsa? Shin Annabi (S) zai iya kwanciya yana barci a jikin wata mace da bincike ya tabbatar ba muharamarsa ba ca? kuma tana cire masa ƙwarkwata?
Shin Ina matsayin kyawawan ɗabi’u da tarbiyyar da AlƘur’ani ya tabbatar masa?
Shin Ina darajar Annabta da ke lazimta samuwar kariya daga dukkan aiki abin zargi?

Matsayar wasu Malaman daga Ahlussunna a kan wannan hadisin:

1-Imam Nawawi: (Sharh Sahih Muslim, juzu’i na 13, shafi na 63)
Ya yi tawilin wannan hadisin domin tabbatar da ingancinsa ta wannan hanyar: Ummu Haram muharrama ga Manzon Allah (S) ta hanyar shayarwa, kuma tsohuwa ce da ba a zaton sha'awa a kanta. (Don haka, hadisin ya halatta a iya jinginawa Annabi).
Ishkalin da zai bijiro a kan wannan tawili na Imam Nawawi shi ne: na farko babu wata hanya data tabbatar da cewa Ummu haram sun sha nono tare da Manzon Allah da har zata iya zama muharrama a gare shi, Abu na biyu kasancewarta tsohuwa mara sha’awa, ko ba tsohuwa ba, hakan baya fitar da ita daga kasancewarta Muharrama ba, abu na uku Nawawi me yasa baiyi magana a kan jingina samuwar kwarkwata a jikin Annabi ko a kansa jingina masa tawaya bane.
.................
Mansur Yahya Bargi 13-7-2025

11/07/2025

WANENE YAKE KAN GASKIYA? (3)

A lokacin da Umar ɗan Abdul’aziz yake rubuta wasiƙar farkarwa da neman a zo a fara tattara hadisai daga Sahabban da s**a rage da wasu daga Tabi’ai, su kuma Imaman Ahlul bayti (a.s) sun yi nisa wajen ilmantar da Al’umma haƙiƙanin ilimi daga gidan Annabta, k**ar yadda ya faro tun daga Imam Ali, sannan wannan yanayin da zamanin na Umar ɗan Abdul’aziz ya baiwa musamman Imam Muhammad Al-Baƙir da Imam Ja’far Al-Sadiq (a.s) damar horar da ɗalibai da dama, kuma s**a bar hadisai ingantattu waɗanda suke tiƙewa kai tsaye ga kakansu (s) hadisai masu tarin yawa waɗanda ake dogara da su har zuwa yau a makarantar Ahlul bayt (a.s)
Daga cikin mashahuran ɗaliban Imam al-Sadiq (a.s) akwai Abu Hanifa, wanda ya kafa mazhabar Hanafiyya, da kuma Maliku bin Anas wanda ya kafa mazhabar Malikiyya. Wadannan malaman fikihu sun karɓi ilimi da yawa daga Imam al-Sadiq (a.s), musamman a fannin usul da fahimtar hadisi da fiƙihu.
Amma shin su waye s**a fara hana jama’a naƙalto hadisan da Ahlulbayt s**a ji daga kakansu Manzon Rahama (s)
Masarautar Banu Umayya waɗanda s**a kasance ɗauke da dakon ƙiyayyar Ahlul Bayt (a.s) tun farkon aiko Annabi (s), sun hana bayyana hadisai daga gare su. Misali, Abdul Malik bn Marwan da wasu sarakunan Umayyawa sun hana masu riwaya su ambaci wani abu daga Ahlul Bayt. Sun faɗa wa masu ruwaito hadisai cewa: “Ba ku da izinin ruwaito wani abu daga Ahlul Bayt.”
Mazhabobi huɗu:
A wannan yanayi ne Abu Hanifa ya kasance yana goyon bayan Ahlul Bayt, amma saboda tsoron tsangwama daga al-Mansur al-Dawaniƙi (sarkin Abbasiyya), bai bayyana soyayyarsa da biyayyarsa gare su a fili ba. don haka, ya kafa makarantar koyarwa inda ɗalibai da yawa, kuma ya zama suna bin fatawowinsa da ra’ayinsa. Sai ya zama ana musu laƙabi da Hannafawa, wato ƴan mazhabar Hanafiyya. Mabiyansa suna da ra’ayin cewa hanya mafi inganci ta zuwa ga sunnar Manzon Allah (S) ita ce ta hanyar fahimta da koyarwar Abu Hanifa.
Bayan Abu Hanifa, sai Maliku ɗan Anas ya kafa majalisar karatu da fikihu, inda yake bayar da fatawowi bisa tushen Alƙur’ani, hadisi, sunnah, ijma’i, da kuma ra’ayinsa abinda a ke kira a Isɗilahin Ilimin Fiƙhu da (ra’yul-faƙihi). Dalibai da yawa s**a bi shi, s**a kuma karɓi fatawarsa, daga bisani aka fara kiransu da ƴan mazhabar Malikiyya. Mazhabar Malikiyya ta samu karɓuwa sosai a wasu yankuna, amma a binda yake a bayyane shine cewa ra’ayoyin Imam Malik da tafarkinsa a wajen fassarar hukuncin Alƙur’ani da Sunnah sun bambanta da ra’ayoyi da tsarin Abu Hanifa.
Daga nan sai Muhammad bn Idris al-Shafi’i wanda da farko ya koyi ilimi daga ɗaliban Abu Hanifa, wanda za mu iya kiransa da jikan Imam Ja’afar (a.s) domin ya yi karatu ne a wajen ɗalibin Imam Sadiƙ (a.s), sai daga baya ya kafa makarantar fatwa da ra’ayi, inda mabiyansa s**a kasance sanannu da suna Shafi’iyyah.
Bayan shi, sai Ahmad ɗan Hambal wanda shima ya yi karatunsa a wajen waɗancan da s**a gabata, ya samu matsayi a fagen fatawa da koyarwa, inda mabiyansa aka sansu da Hanabilah (mazhabar Hanbali).
Dukkan waɗannan mabiyansu sun yi imani da cewa hanya mafi inganci wadda zata kai su zuwa ga fahimtar sunnar Annabi (S) ita ce hanyar waɗancan malaman nasu guda huɗu.
Amma a gefe guda kuma, mabiyan Ahlulbayt (Shi’a) suna da yaƙinin cewa hanya guda da ta fi dacewa wajen fahimtar sunnar Annabi (S) da ra’ayoyinsa ita ce ta Ahlul Bayt (a.s), wadanda Annabi ya bari a matsayin jagorori ga al’umma bayan rasuwarsa a bisa nassi ingantacce daga Manzon Allah (S) kuma hadisan na nan a cikin littafan shi’a da sunna.
Saboda haka, a bisa bayanan da za su zo a nan gaba mai karatu zai fahimci cewa: waɗannan mazhabobin huɗu na Ahlus-Sunna, sun bi hanyoyinsu ne bisa ra’ayoyinsu da fahimtarsu domin kaiwa ga Sunnar Manzon Allah (S). Amma da a ce tun a farkon zamanin Musulunci an aiwatar da wasiyyar Manzon Allah (S) k**ar yadda ya fada, da yanzu ba za a sami mazhabobi daban-daban ba. da dukkan al’ummar Musulmi za su kasance a kan mazhaba guda, hanya guda, da tafarki guda. Kuma da wataƙila waɗanda s**a kafa waɗannan mazahabobin huɗu sun zama wakilai ne na Imaman Ahlul Bayt (a.s) a yankunansu, suna jagorantar mutane da fahimta da tsari iri ɗaya daga gidan Annabta.
........ Mansur Yahya Bargi
11/7/2025

https://www.facebook.com/share/1HRuCGfo7h/

10/07/2025

MUTUM DA KAMALARSA (1)

SHIMFIƊA:
Daga cikin abubuwan da s**a fi daukar hankali a cikin rayuwar mutum akwai tambayar: Shin menene ainihin k**alar ɗan adam a wannan rauywar, wanne matsayi ne mutum zai kai a ce ya kai ga k**ala? Wato me ke sa mutum a ce ya kai matsayi mafi girma a cikin halittarsa? Shin k**ala tana nufin samun ilimi ne kawai, tarin dukiya kawai, kaiwa ga wani matsayi ko shahara a cikin mutane, ko kuwa ta haɗa har da ɗabi’u kyawawa, ko kasancewar mutum mai addini da tsarkakakkiyar zuciya a tsakanin mutum da mahaliccinsa da sauran abokan halittarsa?
Wannan tambayar ba sabuwa ba ce a cikin zukatanmu, kuma tuni addinai da masana falsafa da manyan malamai sun tattauna ta cikin tsawon ƙarnuka. Cikinn amincewar Allah a cikin wannan ɗan rubutun, za mu yi nazari kan mutum da k**alarsa daga mahangogi huɗu: hankali, ilimin addini dana zamani, da ɗabi’ar rayuwa.
Da farko kalmar “k**ala” a Larabci na nufin cikawa, kammaluwa ko kai wa ga matakin da babu giɓi a cikinsa. A Hausance, ana fassara ta da “cikawa ko k**ala” k**ar ayar ƙarshe data sauka a cikin Alƙur’ani mai girma wadda take abinda ya faru ya zama shine sababi na saukarta to da wannan abun ne Addinin Musulunci yake cika wato yake kaiwa ga k**alarsa a wurin Allah. To idan aka ce mutum ya kai ga k**alarsa, ana nufin ya kai wani matsayi na ƙololuwa a cikin abinda yake shine mafi darajar da yasa a ka halicce shi ko da shi ne yake zama cikakken mutum.
Kamala tana shafar nau'ikan rayuwa daban-daban misalin:
Kamalar ilimi: samun fahimtar gaskiya da aiki da shi.
Kamalar ɗabi’u: kiyaye halaye masu kyau k**ar gaskiya, riƙon amana, adalci, tausayi da haƙuri.
Kamalar zuciya: tsarkake ta daga son rai da ganin kai ako yaushe, hassada, zargi, ƙiyayya, da aikata zunubai.
Kamalar imani: kusantar Allah ta hanyar ibada da amincewa da hukuncinsa.
Kamalar jagoranci: adalci, haɗa kan mabiya da gaske, cicciɗa al’ummar da ake jagoranta zuwa cigaba a addini, ilimi, da tattalin arziƙi. Da sauransu
To kuma tunda Aƙida tana da matuƙar muhimmaci cikin aiyukan da suke gangarowa a rayuwar mutum, to wajibi ne yin amfani da hankali da hikima da binciken neman gaskiya a wajen zaɓar aƙida ta kwarai,-wadda ta ginu akan asasin hujjoji daga Alƙur’ani Mai girma da Sunna Maɗaukakiya da hankali- saboda tabbas zaɓar kowace irin aƙida ko tunani yana da matuƙar tasiri a makomar mutum. Za a iya cewa dukkan wasu ɗabi'un da ka ga mutum yana yi, to sak**akon irin fikirarsa ne wato (theory of knowledge)
Za a iya cewa ma halayyar da ɗan’adam ke yi sak**akon irin abin da ya yi imani ne da shi, kuma shi yake bayyana a zahiri. Asalin bambamci na tushe da ake samu a tsakanin mutanen ƙwarai da waɗanda ba su ba, yana koma wa ne zuwa ga bambancin abinda s**a yi imani da shi a zukatansu da tunaninsu ne. Don haka ne ma AlƘur'ani Mai Girma yake matuƙar yin kira ga mutum zuwa ga zurfafa tunani da zaɓin tafarki mafifici, da ingantacciyar aƙidah da riƙo da abinda ya kai zuwa gare shi ta hanyar Ilimi da bincike ba wai zato ko gado ba. Shi ya sa ma ya kasance mafi munin halittu a wajen Allah sune mutanen da aka siffanta su da kurame kuma bebaye wato waɗanda kwata-kwata ba sa hankalta.
Don haka, kafin komai dole ne mutum ya mayar da hankali ya yi tunani da bincike mai zurfi a kan abin da shine rayuwarsa ta ginu a kai a asasi.

.............
Mansur Yahya Bargi
10-7-2025

https://www.facebook.com/share/1HRuCGfo7h/

Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Address

Kano