09/08/2026
Alhamdulillah!
A jiya Asabar Baban Malamin Mu Sheikh Abubakar Salisu Sharfadi ya kammala karantar da littafin Hakokin Mata Akan Maza, wanda yake gabatarwa duk ranar Asabar bayan Sallar Magariba zuwa Isha’i a Masallacin Sheikh Ja’afar M Adam, Sharada. A cikin darussa 28.
Darasi ne mai matuƙar amfani kan haƙƙoƙin mata, kyakkyawar mu’amala tsakanin ma’aurata, soyayya, rahama, haƙuri, kyawawan ɗabi’u da yadda ya kamata musulmi ya gina gidansa bisa shiriyar Al-Qur’ani da Sunnah. Littafin ya kuma nuna mana cewa gyaran gida da zaman lafiya tsakanin ma’aurata na daga cikin manyan abubuwan da ke taimakawa wajen gyaran al’umma.
Manufar marubucin littafin ita ce ya taimaka wajen gyaran rayuwar aure da dawo da kyakkyawar mu’amala da koyarwar Annabi ﷺ a cikin gidajen Musulmi
Allah Ya sa abin da aka karanta ya zama sanadin gyaran gidajenmu da kyautata zamantakewarmu.
Insha Allah, daga Asabar mai zuwa za'a ci gaba da wani muhimmin littafi:التحصينات الإيمانية من المداخل الشيطانية na Sheikh Wahid bin Abdul-Salam Bali. Wannan littafi yana magana ne kan hanyoyin da shaidan yake bi wajen karkatar da mutum, da kuma irin kariyar imani da musulmi yake bukata domin kare kansa daga waswasin shaidan da dabarunsa. An riga an fara wannan littafi, kuma an gabatar da darussa 10 kafin a dakata; yanzu kuma lokaci ya yi da za a dawo a ci gaba daga inda aka tsaya.
Don haka, ɗalibai da masu kishin ilimi kada ku rasa wannan cigaba! Littafin ya shafi wani muhimmin al’amari da kowane musulmi yake bukatar fahimta, domin sanin makircin maƙiyi shi ne mataki na farko wajen kare kai daga cutarsa.
Mu kasance tare da Malam daga Asabar mai zuwa, domin mu ci gaba da neman ilimin da zai ƙara ƙarfafa imanimmu, ya gyara rayuwarmu, kuma ya taimaka mana wajen kare kanmu daga hanyoyin shaidan. Allah Ya sa mu amfana da ilimin da muke koya, Ya ba Malam lafiya da ikon ci gaba da wannan aiki na alheri. Amin.
Ishaq Shuaibu Ibrahim
SunnahOnline24