Fatihu Sabiu

Fatihu Sabiu

Share

Sharing factual, enlightening and beneficial content to the public.

08/04/2024

DOGARO DA ILIMIN FALAKI WAJEN TABBATAR DA GANIN WATA.

Babban Malamin nan Ash-Shaikh Bakar Abdullah Abu Zaid Allah Ya yi masa Rahama, cikin kyakykyawan littafin nan na sa wanda ya ke magana a kan sababbin mas'aloli a Addini, wato (فقه النوازل) Ya yi bayanai masu kyau, bayanai na ilimi, bayanai gamsassu, a kan sha'anin aminta da dogara da maganar masana ilimin falaki (Astronomy) wajen tabbatar da ganin Wata.

Malamin ya kai matuka wajen bayanin wannan mas'ala yadda ya kamata. A cikin bayanansa a wanann Littafi ya kawo misalai na irin yadda sau da yawa ake samun tasgaro da cikas da rashin tabbaci cikin bayanan masu wannan ilimi, inda ya nuna cewa maganganun masu ilimin falaki wajen tabbatar da ganin wata ba wasu maganganu ba ne tabbatattu yanke! Kuma Shari'ar Musulunci ba ta yi Umarni da a dogara a kansu kacokam ba! Ta yadda idan sun fadi abu, to shike nan ya zauna daram dam!!! Ya tabbata. Ya ce sau da yawa suna kore yiyuwar ganin wata, amma kuma sai a samu an gan shi a wasu kasashe daban-daban, ta hanyar amintattun mutane masu yawa. Wanda hakan ke nuna maganarsu ba Yakini ba ce, kuma za su iya fad'a a samu sabanin abin da s**a fad'a, sannan ba za a karyata amintattu ba a kan kawai bincikensu wanda zai iya zama daidai, zai iya zama kuskure, ko za a iya samun chanji daga bayan binciken na su.

Hakika yadda wannan Bajimin Malamin Duniya Shaikh Bakar Abu Zaid ya yi bayanin wannan mas'ala filla-filla ya kayatar da ni, maganganunsa akwai bincike da zurfin ilimi da nufatar daidai, Kuma wannan shi ne abin da ya kamata a rike a a matsayin abin lura a cikin wannan mas'ala.

Domin kuwa da ma wannan ita ce Matsayar daukacin malaman musulunci tun a baya, da kuma a yanzu, ba a zallar dogaro da maganar masana ilimin Falaki wajen lissafin ayyukan Ibada.

Kafin Sheikh Bakar Abu Zaid, shi ma Shaikhul Islam Ibn Taimiyya ya yi bayani mai fad'i a kan wannan mas'ala cikin "Majmu'ul Fatawa" Juz'insa na (25) haka nan Alhafiz Ibn Hajar a cikin "Fat'hul Bari" da kuma sauran ma'abota ilimi tun a zamunan baya.

Don haka cin fuska ne, azarbabi ne wani masanin ilimin Falaki (Astronomer) ya fito yana hakikance cewa dole Azumi (30) za a yi, yana mai jazami da tabbatar da cewa ala dole tilas ba zai tab'a yiyuwa a ga jinjirin watan Shawwal a ranar (29) ga Ramadan ba, duk wanda ya ganshi Karya ya ke! Duk wadanda s**a gan shi s**a yi Sallar Idi a washegari sun sha Azumin Ramadan, sun afka Zunubi! Wannan ba daidai ba ne! Kuma ba Yakini ba ne!

Asali a Shari'ar Musulunci shi ne duba na ido, kamar yadda Ayar Alkur'ani da Hadisan Annabi (S.A.W) s**a tabbatar. Don haka in dai amintattu s**a tabbatar da ganin wata, babu Hujjar da za ta sa a kore ganinsu ko a musanta shi saboda binciken wasu wanda ba Yakini ba ne. Lissafi ne, zai iya zama gaskiya, zai iya zama da kuskure a cikinsa. Haka nan idan aka biyewa wannan Kofa, to ana nan ma za a rufe batun gani da ido din kacokam! A koma kawai ga yan ilimin Hai'ah wajen duba wata.

Karin Bayani: Hikimar wannan Rubutu shi ne haskakawa domin komawa wadannan littafai da na ambata a ga mai malamai s**a yi bayani a kan wannan batu, sannan kuma a gurguje a wanke zukatan wasu daga rudanin da wadancan masanan ilimin falakin ke jefawa al'umma duk Shekara.

A karshe, muna tare da abin da Sarkin Musulmi ya yi umarni, muna bisa abin da sanarwarsa ta hukunta, kuma mu sani Sarkim Musulmi bai dogara da maganganun wadancan mutane ba kacokam! Domin idan da ya biye ta tasu, ya dogara da su, to ba ma za a umarci mutane su duba wata ba a yau Litinin (29) Ga Ramadan, kai tsaye za a fitar da sanarwa ne cewa Azumi (30) za a yi, yin Sallar Idi sai ranar Laraba kawai. Amma ga shi an fitar da sanarwar cewa al'umma su duba watansu a yau (29) ga Ramadan, daga nan kuma sai a bi matakai na tantancewa yadda aka saba. Allah Ya sa mu dace, Ya dora mu a kan abin da ya ke shi ne daidai.

Mai Rubutu:
Musa Muhammad Dankwano
29-Ramadan-1445

07/04/2024

Babban Malaminmu Asst. Prof. Sheikh Bashir Aliyu Umar OON (Hafizahullah) tare da Baffa Mahaifinsa mai girma Dan Amar na Kano Allah Ya kara masa Lafiya a yau (28) Ga Ramadan a yayin rufe Majalisin Tafsirin na wannan Shekara ta (1445)

Babban Malamin ya yi Tafsiri mai ban kaye cikin Suratul Ahzab, in da aka fitar da zunzurutun fikihu da fa'idoji na ilimi a cikin wannan Sura mai Albarka. Lalle masa'il din da aka tattauna a wadannan majalisai Dalibi na da bukata komawa ya saurare su a nutse.

Allah Ya saka wa Malamanmu da Alkhairi Ya kara musu Lafiya da Albarka.

Musa Muhammad Dankwano
28-Ramadan-1445.

30/10/2023

This 3millionTT program under NITDA was lunched some weeks ago and the status of the application suggests that people from the North are left behind.

When they release list of successful candidates with people from the North lagging behind, it will now become a regional or tribal fight unnecessarily despite the fact that we neglected it.

NITDA can not force anyone to apply nor can they shortlist anyone without application. They have done their part by publicizing it. Its now left for us to apply or look away. Looking away comes with consequences.

And let's know that the more people apply the more chances of more people getting shortlisted.

Let's encourage our family and friends to seize this opportunity.

Share for others please 🙏

STEPS TO APPLY IN THE COMMENT SECTION 👇

30/10/2023

"If Atiku, Obi contest again in 2027, they will lose."

– Reno Omokri

Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Website

Address


Kano