Ahbabu Rasulullah Kumbotso

Ahbabu Rasulullah Kumbotso

Share

Gida ne Domin Tsantsar Masoya Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam. Munayin Mauludi kuma Rera Yabo

24/04/2026
14/04/2026

Kamar yadda bazaka iya kamo rana da hannunka ba, haka nima bazaka iya kamo ni a Soyayyar Manzon Allah ba.

~Shiekh Ibrahim Inyass.

13/04/2026

Kaunar Annabi Alaihissalam idan muka sakata agaba duk abinda ya damemu Allah sai ya warware mana.

~Prof. Umar Sani Fagge.

13/04/2026

Duk wanda zai sawa dansa suna Muhammad sai ya kula wajen fadar sunan saboda sunan akwai daraja.

~Prof. Umar Sani Fagge

12/04/2026

Duk yadda kake da zafi kan akidarka, ka tsaya ka fahimci wannan karatun, kada malamanka su kai ka ga halaka.

‎Wasu sukan yi ƙarya su ce Shehu ya yi iƙirarin matsayin da ya wuce na ɗan adam ko kuma ya sanya kansa a matsayin da ya saba wa koyarwar Musulunci.

‎Akwai masu yi masa sharri suna cewa dukkan koyarwarsa bidi’a ce, alhali tushenta Alƙur’ani ne da Sunnar Manzon Allah (S.A.W).

‎Sukan ɗauki sashen maganarsa su yanke ta yadda za ta ba da ma’ana mara kyau, domin kawai su ɓata masa suna a idon duniya.

‎Wasu sukan ƙirƙiri maganganu su jingina su gare shi, suna cewa daga littattafansa ne, alhali bai taɓa faɗar hakan ba, kuma ba ya cikin sahihan rubuce-rubucensa.

‎Wasu kuma sukan yi zargin cewa ya zo ne don raba kan Musulmi, alhali tarihin rayuwarsa duka kira ne zuwa ga haɗin kai da ƙaunar juna.

‎Suna ƙoƙarin siffanta shi da abubuwan ƙarya domin rage darajarsa a zukatan matasa da masu tasowa.

‎An yi masa ƙage kan matsayinsa, ba mu yafe ba.

‎An yanke maganganunsa domin a ɓata masa suna, Allah zai bi mana haƙƙinmu.

‎An ƙirƙiri ƙaryar cewa koyarwarsa bidi’a ce, alhali duka Sunna ce.

‎An jingina masa littattafan da bai rubuta ba domin a yaudari mutane.

‎An siffanta shi da raba kan al’umma, alhali shi jagoran haɗin kai ne.

‎Duk wanda ya ce zai toshe hasken Shehu da bakinsa, Allah zai kunyata shi.

11/04/2026

Duk wanda zai sawa dansa suna Muhammad sai ya kula wajen faɗar sunan saboda sunan akwai Daraja.

11/04/2026

Duk abin da mutum yake so a duniya, akwai ranar da zai rabu da shi. Amma soyayyar Manzon Allah (S.A.W) ita ce kaɗai jarabtar da take kai mutum ga babban rabo a duniya da lahira.

Kamar yadda Shehu (R.A) ya faɗa, kowa da abin da aka jarabce shi da so. Shin kai mene ne naka babban burin a rayuwa?

17/03/2026

اللهم انك عفو تحب العفو فعف عنا

27/12/2025

Ga mutanenfa sun dakko karatu

Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address

Kumbotso
Kano