Amb. U M Hussaini

Amb. U M Hussaini

Share

Motivated & results-driven professional with experience in content creation, research, analysis & organizational management. Usman studied B.Sc. (Ed.)

Proven track record in leading teams, driving strategic growth & fostering collaboration, passionate advocate for serving humanity Usman Mallam Hussaini hails from the Capital City of Kano, Nigeria, he is an indigene of Gwale LGA of the State. Health Education at Bayero University, Kano (BUK), and currently a postgraduate student who studies M.Sc. Public Health at National Open University of Niger

16/02/2024

Allah ka sanya mu, kuma ka tabbatar damu a masu aikata ayyuka na ƙwarai da hidimtawa al'umma. Allah muna roƙonka da sunayenka kyawawa, ka bamu juriya da jajircewa kan gaskiya da taimakon gaskiya a ko wane hali, duk wuya duk rintsi. Allah Ka ƙarawa Annabi ﷺ daraja.

~ U. M. Hussaini (16/02/2024).

02/02/2024

Allah ka kawo mana sauƙi a wannan rayuwa, abin da ya fi ƙarfinmu, Allah kasa mu fi ƙarfinsa. Ya ubangiji duk abin da za muyi dana-sanin yinsa, Allah ka hana mu aikata shi. Allah ka rabamu da ƙunci, da talauci, ka tabbatar da mu kan ayyuka na ƙwarai albarkar Annabi Alaihis-Salam.

© U. M. Hussaini (02/02/2024).

26/01/2024

Allah ka rabamu da zalinci, da ƙyeta, da cin amana. Ubangiji ka tabbatar damu kan aikata adalci, da tausayi, da gaskiya, da riƙon amana, albarkar Annabi Alaihis-Salam.

BARKA DA JUMA'A!

© U. M. Hussaini (26/01/2024).

19/01/2024

Allah Ka saukar da rahama, da salaama, da arziƙi, da watada, da dukkanin alkhairan duniya da na lahira a kanmu da masoyanmu. Ubangiji muna roƙonka da ka kiyayemu da kiyayewarka, ka dafa mana da dafawarka, Allah ka tabbatar damu akan ayyukan alkhairi, mu yi su a cikin nishaɗi da walwala, ba tare da gajiyawaba albarkar babban masoyinka Annabi Alaihis-Salam.

BARKA DA JUMA'A

© U. M. Hussaini (19/01/2024).

26/08/2023

RANAR HAUSA

Tasirin haɗuwar al'umma baya yiyuwa har sai mutane sun shirya kansu tareda tsayawa kan manufofi da kuma girmama dokoki ko yarjejeniyar haɗuwar tasu.

Waɗansu daga manyan abubuwan da suke kassara haɗuwar kan al'umma da samun natijar haɗudar sun haɗa da: ƙiyayya, ƙyama, hassada, zalinci da son zuciya.



© U. M. Hussaini (26/08/2023).

30/04/2023

Kafin ka zargi mutum akan cewa baiyi daidai ba, wanne gudun mawa ka bashi domin ya fahimci daidai ɗin tukunna?

Mutane suna manta nauyin dake kansu, sai su tafi lalubo kusa-kuren wasun su. Lallai al'ummar mu na buƙatar saiti.

© U. M. Hussaini (30/04/2023)

30/04/2023

Yawaita magana mara amfani babban dalili ne na zube war mutunci, domin mai yawan surutu barkatai ya na iya furta kalaman da za su zubar masa da ƙima ba tareda ya san haka ba.

Sau da dama akan samu tufka da warwara cikin kalaman mutane masu yawan surutai barkatai. Ku taƙaita magana ko domin saboda tsare mutuncin ku a idanun mutane masu daraja.

© U. M. Hussaini (25/04/2023)

24/04/2023

Gwamnati ga yayan ki suna roko, a taimaka musu

24/04/2023

Gwamnati ki taimaki yayan ki.

23/04/2023

Hassada mugun ciwo ne, mai Hassada baya taɓa samun sukuni da nutsuwa a zuciya, musamman wajen gudanar da al'amuran Rayuwa kamar yadda sauran mutane ke yi.

Daga cikin illar Hassada, ku lura sosai, duk wani saɓani, rikici ko rigima dake tsakanin mutune (mai alaƙa da Hassada) ba'a taɓa denawa, sai dai a samu lafawa. Koda an sasanta tsakani, wata rana sai wanda yake da tsananin Hassadar ya taso da fitana (a wani salo na daban).

Matuƙar akwai ɓarɓashin Hassada a zukatan mutane, to zaku tarar cewa babu zaman lafiya a inda masu Hassada ke zaune. Ana samun zaman lafiya ne kawai idan aka rasa abunda zasu yiwa hassada.

© U. M. Hussaini (23/04/2023)

21/04/2023

EID AL-MUBARAK & JUMA'AT AL-KAREEM!
اَلسَلامُ عَلَيْكُم وَرَحْمَةُ اَللهِ وَبَرَكاتُهُ‎:

A wannan rana ta Juma'a mai tarin albarka da falala, a madadi na da iyalai na, ina yi muku barka da Sallah, tareda fatan Allah Ya karɓi ibadun da muka gabatar a wannan Wata na Ramadan.

Muna addu'ar Allah (SWT) Ya sada mu da Alkairan da ke wannan Shekara, Sharrin da ke tattare da Shekarar kuma Allah Ya kare mu. Ubangiji Ya cigaba da rufa mana Asiri Duniya da Lahira albarkar Annabi (ﷺ) da Iyalan Gidansa tsarkaka.

© U. M. Hussaini (21/04/2023).

06/04/2023

Ba a fahimtar da mutane Addini ko Gaskiya ta hanyar tunzura jama'ar gari, ballantana a shigar da Gwamnati cikin mas'aloli waɗanda hujjatayya suke buƙata.

Wanda ya dage sai ya lalubo laifi ko raunin ka saboda ƙiyayya, ba zaka taɓa yin daidai a wajen sa ba. Koda iyayen sa ka taimaka, sai yace kana wulaƙanta masa iyaye. - U. M. Hussaini

Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Address

Kano