03/01/2023
YADDA MAKARANTAR AS'HABULKAHFI TA CANJA NI BAYAN NA TSINCI KAI NA A CIKIN TA, ALHAMDULILLAH !!!
Saifullahi Murtala Jibia
* YIN ADDINI BABU HANKALI ZUWA YIN ADDINI BISA DORON HANKALI.
* ADDINI BISA NASSI/HUJJA TARE DA SAUKA DAGA ABIN DA YA SAƁA DA NASSI/HUJJAR, KO DA KUWA CIKIN SA AKA HAIFE NI.
* ADDINI DA ƘIN AHALIN GIDAN ANNABI (SAW) ZUWA YIN ADDINI DA ZAZZAFAR ƘAUNAR AHALIN GIDAN ANNABI (SAW) WATO (AHALILKISA'I).
* ADDINI BISA SON/ƘAUNAR WAƊANDA S**A KARKASHE JIKOKIN ANNABI SAW ZUWA YIN ADDINI BISA MASIFAFFIYAR ƘIYAYYA KUMA ZAZZAFA,GA WAƊANDA S**A KASHE AHALIN GIDAN MANZON ALLAH (SAWW), TA HANYAR SHAYAR DA SU GUBA, DA KUMA CIRE MASU KANU.
* YIN ADDINI BISA YARDA TARE DA ƊA'A GA WANDA YA SAƁA DA ANNABI (SAW), ZUWA YIN ADDINI BISA ƘIN YARDA DA ƊA'A, GA DUK WANDA YA SAƁA DA ANNABI (SAWW) KO DA SAHABI NE, KOWAYE (( ANNABI (SAW) YA FI SHI ))
* YIN ADDINI BISA GANIN DUK WANDA BA ƊAN ƘUNGIYATA BA ƁATACCE NE, ZUWA YIN ADDINI BISA CIGIYAR GASKIYA A DUK INDA NA SAME TA, DA AIKI DA ITA. TARE DA NISANTAR ƘARYA A DUK INDA NA GAN TA,KO DA KUWA A CIKIN ƘUNGIYA TA CE.
* YIN ADDINI BISA RASHIN GIRMAMA FAHIMTAR WASU TARE DA AIBATA SU, ZUWA YIN ADDINI BISA GIRMAMAWA GA FAHIMTAR WASU, TARE DA YI MASU FATAN ALKHAIRI A CIKINTA.
* ADDINI BISA YARDA DA HADISAI MA SU TAWAYE MUTUNCIN ANNABI (SAW) ZUWA YIN ADDINI BISA ƘIN YARDA DA DUK WANI HADISI WANDA KE TAWAYE MUTUNCIN ANNABI (SAWW) KOWA YA RUWAICE SHI, KUMA KO CIKIN WANE LITTAFI YAZ ZO.
ذَالِكَ فَضْلُ اللَّهِ يُؤْتِيهِ مَنْ يَشَـــــــــــاءُ وَاللَّهُ ذُالْفَضْلِ الْعَظِيمِ
ALHAMDULILLAH, INA TARE DA SARKIN GIDAN MALAM KABARA, MUJADDADIN ADDINI NA WANNAN ƘARNI, MAULANA DR. SHEIKH ABDULJABBAR KABARA (H) JASADAN WA RUHAN.
🇳🇬 AS'HABULKAHFI JIBIA SOCIAL MEDIA TEAM, 03/01/2023 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
29/12/2022
DADDATSA NAMAN MUTUM YAKAMATA A YI WATO (MISLÃ) IDAN HAR YA KUMA CEWA AN TSÃGA ƘIRJIN ANNABI (SAW) AN FIDDO MASA ƘAZANTA, BÃ WAI IYÃ KISA BA KAƊAI !!!
✍️ Saifullahi Murtala Jibia
Waɗanda ba musulmi ba, suna iya cewa mun zama mahaukata idan muka yarda cewa, maɓallin rigar Annabi ya fi zuciyar Annabi (saww) daraja kamar yadda yake rubuce a litattafan mu na muslinci !!! To ya abin shike ne ????
* MATSAYIN MAƁALLIN RIGAR ANNABI (SAWW) A GURIN MUSULMI !!!
Girman darajarsa tã kai idan har mutum ya kuskura ya ce yana da datti ( ƙazanta) to hukuncinsa kisa ne.
Babban Masoyin Manzon Allah (saww) wato Imamuna Alƙadi (Mai Kitãbusshifã) ya kawo wata magana wacce zan yi nuni da ita a cikin littafinsa mai albarka a cikin waɗannan gurare :
القسم الرابع ( فِي تَصَرُّفِ وُجُوهِ الْأَحْگامِ فِيمَنْ تَنَقَّصَهُ أَوْ سَبَّهُ صلي الله عليه وسلم)
الفصل الأول: الْحُكْمُ الشَّرْعِيُّ فِمَنْ سَبَّ النَّبِيُّ صلي الله عليه وسلم ، أَوْ تَنَقْصَهُ
Fasali na farko : Mai bayanin hukuncin da shari'a ta yanke a kan wanda ya zagi Annabi (saww) ko ya tawaye darajar sa.
A kan hanyar Imamuna Alƙadi (R)ta kawo maganganun Malamai, da ijma'in su ne ya haikaitar da wannan :
وَرَوَى ابْنُ وَهْب عَنْ مَالِكٍ : مَنْ قَالَ : إِنَّ رِدَاءَ النَّبِي صلي الله عليه وسلم ، وَ يُرْوَى زِرَّ النَّبِيِّ صلي الله عليه وسلم وَسِخٌ ـ أرَادَ بِهِ عَيْبَهُ قُتِلَ.
Ibn Wahbin ya ruwaito daga Malik cewa : Wanda ya ce " lallai bargo/mayafi/tufafin Annabi, ko aka ruwaito ya ce Maɓallin rigar Annabi (saww) yana da ( dauɗa ) wato datti, da nufin aibata Annabi (saw) to A KASHE SHI !!!
To tunda hukuncin wanda ya ce maɓallin rigar Annabi (saww) yana da datti (dauɗa) A KASHE SHI, mene ne hukuncin wanda ya ce ZUCIYAR ANNABI (SAW) TANA DA DATTI, (DAUƊA) KUMA SHAIƊAN NE KE SAKA MASA ITA ????
Maɓalli dai bai kai darajar tufafi ba, tufafi kuma bai kai darajar gangar jiki ba, ita kau gangar jiki , ba ta kai darajar zuciya ba. Domin kuwa, ita zuciya ita ce sitiyarin da ke tuƙa gangar jikin Ɗan'adam, idan har ta gy