Markazu Amãnil Jamiy

Markazu Amãnil Jamiy Cibiyar Da'awar Salafiyya Zalla
(Domin yin Wa'azi da kuma karantar da Tauhidi, Manhaji da Aqidar Musulman Farko).📚📖📚

RATAYA AYA KO SURAR ALQUR'ANI A BANGO BID'AH NE(Fatwar Sheikh Ibnu Uthaymeen – Allah Ya yi masa rahama)-Daure ka karanta...
18/07/2026

RATAYA AYA KO SURAR ALQUR'ANI A BANGO BID'AH NE
(Fatwar Sheikh Ibnu Uthaymeen – Allah Ya yi masa rahama)

-Daure ka karanta maganarsa gaba ɗaya saboda yawan amfanin da take ƙunshe da shi-

Jiya Juma'ah muka ga wani Ɗan Media ya yaɗa hoton Malam Kabiru Gombe da Ɗansa, ajikin hotunan sai aka hango Suratu Yasin an rataye ta a bango, shine muke tura wannan a matsayin nasiha ga kanmu da Malam da kuma duk wanda saƙon yaje masa.

Acikin Fatāwā Nūr 'Alā Ad-Darb Al-Imam Ibnu Al-Uthaimin (Allah ya jikansa) yace:

"Rataya ayoyin Alƙur'ani a bango, ko ƙofofin masallatai, da makamantan wurare, yana daga cikin sabbin abubuwan da aka ƙirƙira a addini (bid'o'i),

Waɗanda ba a san su ba a zamanin magabata na ƙwarai (Salafus Ṣāliḥ), waɗanda su ne mafificin al'ummomi.
Annabi ﷺ ya tabbatar da haka inda ya ce:
"Mafificin mutane su ne mutanen ƙarnina, sannan waɗanda suke bayansu, sannan waɗanda suke bayansu."

Da ace wannan abu yana daga cikin abubuwan da Allah Maɗaukaki yake so, da Allah Ya shar'anta shi ta bakin Manzonsa ﷺ.
Domin duk abin da yake amfanar mutane a cikin addininsu da duniyarsu, to Manzon Allah ﷺ ya bayyana shi ya kuma shar'anta shi.

Da wannan abu alheri ne, da Salafus Ṣāliḥ sun riga mu aikata shi.
Sannan ya ce:
Muna tambayar waɗanda suke rataye waɗannan ayoyi:
Me kuke nufi da wannan ratayawar?
Idan s**a ce: Muna nufin girmama Kalaman Allah.
Sai mu ce: Wallahi! Ba mu fi Sahabban Manzon Allah ﷺ girmama Littafin Allah ba. Duk da haka ba su rataye komai daga cikin ayoyin Allah a bangon gidajensu ko bangon masallatansu ba.

Idan kuma s**a ce: Muna son tunatarwa da wa'azi.
Sai mu ce: Mu dubi abin da yake faruwa a zahiri. Shin mutanen da suke ganin waɗannan ayoyin suna wa'azantuwa da su?
Wataƙila hakan yana faruwa, amma yana da matuƙar wuya.

Mafi yawanci abin da yake jan hankalin mutane shi ne kyawun rubutun ayoyin, ko frame ɗin da aka sa musu, ko adon da aka yi musu, da makamancin haka.
Yana da wuya ƙwarai mutum ya ɗaga kansa ya karanta su domin ya yi wa'azi da abin da suke ƙunshe da shi.

Idan kuma s**a ce: Muna neman albarka da su.
Sai mu ce: Wannan ba ita ce hanyar neman albarka ba.
Alƙur'ani gaba ɗayansa mai albarka ne, amma albarkarsa tana samuwa ne ta hanyar karanta shi, fahimtar ma'anoninsa da aiki da shi; ba ta hanyar rataye shi a bango ya zama kamar kayan tarihi da ake kallo ba.

Idan kuma s**a ce: Mun rataye su ne domin kariya da tsari,
Sai mu ce: Wannan ma ba ita ce hanyar kariya ko tsari ba.

Domin azkar da ayoyin Alƙur'ani suke amfani ne ga wanda ya karanta su.

Kamar yadda Annabi ﷺ ya ce game da wanda ya karanta Āyatul Kursiyyu da dare:
"Za a ci gaba da kasancewa yana da mai tsaro daga Allah, kuma shaiɗan ba zai kusance shi ba har ya waye."

Duk da haka, wasu majalisu – ko ma da yawa daga cikinsu – da ake rataye waɗannan ayoyi, ana samun surutu marar amfani a cikinsu.
Har ma ana iya samun maganganu haram, ko waƙoƙin haram. Wannan kuwa yana ɗauke da wani nau'i na wulaƙanta Alƙur'ani ta fuskar ma'ana, abin da yake a bayyane.

Bayan haka kuma, akwai wulaƙantarwa ta zahiri da mai tambaya ya ambata, wato waɗannan takardun suna iya faɗuwa kasuwanni ko wuraren datti, a taka su da ƙafafu. Wannan ma wani abu ne da ya wajaba a tsarkake Kalaman Allah daga gare shi"

Sannan sai Al-Imam ya kammala da cewa:
"Taƙaitawa: Rataye waɗannan ayoyi ya fi kusantar zama sanadin zunubi fiye da samun lada.
Bin hanyar tsira da kauce wa wannan shi ne mafi dacewa kuma mafi cancanta ga muminai.

Bugu da ƙari, na ga wasu mutane suna rubuta ayoyin Alƙur'ani da haruffa masu matuƙar ado, har na ga wasu suna tsara wasu ayoyi cikin sifar tsuntsu, ko dabba, ko mutum zaune irin zaman tahiyyar sallah, da makamancin haka.

Suna rubuta ayoyin ne ta wata hanya haramtacciya, wato hanyar yin hotuna, alhali Annabi ﷺ ya la'anci masu yin irin waɗannan hotuna".

Yaɗawa:
Markazu Amãnil Jãmiy Nigeria

Kuyi share domin saƙon ya yaɗu, Allah Ta'ala yasa daku acikin ladan,
Wassalamu alaikum.

17/07/2026

ALLAH NE KAƊAI ME KARƁAR TUBA -01-
إقامة البرهان على اختصاص الرحمن بقبول التوبة والغفران
(Tsayar da hujja kan cewa Allah Mai Rahma ne kaɗai Ya keɓanta da karɓar tuba da yin gafara)
Raddi ga Kabiru Bashir Abdulhamid (Abu Rumaisah)

SANARWA ! SANARWA !! SANARWA !!!Muna farin cikin sanar daku cewa akwai karatun takarda mai taken:-إقامةُ البرهانِ, على ا...
15/07/2026

SANARWA ! SANARWA !! SANARWA !!!

Muna farin cikin sanar daku cewa akwai karatun takarda mai taken:-
إقامةُ البرهانِ, على اختصاصِ الرحمنِ بقبولِ التوبةِ والغفران
(Tsayar da hujja, akan cewa Allah mai rahma shi kaɗai ya keɓanta da karɓar tuba da yin gafara)

RADDI GA KABIRU BASHIR ABDULHAMID (Hayaƙi fidda na kogo) -Aslahahullah-

🎙 Muhammad Sani Bn Al-Mansoor
(Abu Mufida Assalafiy) -waffakahullah-

Akan Shafin Markazu Amãnil Jãmiy
Ranar Juma'ah 1/2 Safar 1448H
17th July 2026
Lokaci 08:00 na dare

🌙 MAJLISAN WATA 🌙المجالس الشهرية لتعليم اللغه العربيه والعلوم الشرعية Audio !   Audio !!  Audio !!!KARATUN NAHWU DAGA LI...
04/07/2026

🌙 MAJLISAN WATA 🌙
المجالس الشهرية لتعليم اللغه العربيه والعلوم الشرعية
Audio ! Audio !! Audio !!!
KARATUN NAHWU DAGA LITTAFIN:

*AL-AJURRUMIYYAH*
Darasi na 03
https://t.me/MarkazAmaanAljamiyKano/863

📌 Cigaba da bayani game da rabe-raben Li'irabi
📌 Sanin alamomin Li'irabi
📍 Arraf'u
📍 An-nasbu
📍 Al-khafdu
📍 Al-Jazmu

🎙 Muhammad Sani Bin Al-Mansoor
As-salafiy Al-athariy
(Waffakahullah)

Domin ka sami sauran karatuka da shirye-shirye da wallafe-wallafen da ake gudanarwa a wannan cibiya to kabi wannan Link
👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/HiL4A2jWoY5312AsItIB8L

https://t.me/MarkazAmaanAljamiyKano

03/07/2026

IQRA' QIRA'ATIY ONLINE PROGRAM (Shiri na musamman domin masu koyon haɗa baƙi) Darasi na 002
Markazu Amãnil Jamiy Salafiyyah a Nigeria - السلفية في نيجيريا

📌 Hadisai Huɗu Don Samun Mafita Daga Baƙin Ciki da Tsanani❶ Daga Ibn Abbas (رضي الله عنهما), ya ce:Annabi ﷺ idan wani ba...
02/07/2026

📌 Hadisai Huɗu Don Samun Mafita Daga Baƙin Ciki da Tsanani

❶ Daga Ibn Abbas
(رضي الله عنهما),
ya ce:
Annabi ﷺ idan wani baƙin ciki ko tsanani ya same shi, yakan ce:
«لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمُ، لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ رَبُّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَرَبُّ الْأَرْضِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْكَرِيمِ»
Ma'ana:
"Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, Maɗaukaki, Mai Haƙuri. Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Al'arshi Mai Girma.
Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai da ƙasa, kuma Ubangijin Al'arshi Mai Daraja."

📚 Bukhari da Muslim s**a ruwaito.
════🌹════🌹════

❷ Daga Asma'u bint Umays
(رضي الله عنها),
ta ce:
Manzon Allah ﷺ ya ce mini:
«أَلَا أُعَلِّمُكِ كَلِمَاتٍ تَقُولِينَهُنَّ عِنْدَ الْكَرْبِ؟»
Sai ya ce ki ce:
«اللَّهُ اللَّهُ رَبِّي لَا أُشْرِكُ بِهِ شَيْئًا»
Ma'ana:
"Allah! Allah ne Ubangijina, ba na haɗa Shi da wani cikin bauta."

📚 Abu Dawud ya ruwaito, Al-Albani ya inganta shi.
════🌹════🌹════

❸ Daga Abu Bakrah
(رضي الله عنه)
Annabi ﷺ ya ce:
Addu'ar wanda yake cikin damuwa ita ce:
«اللَّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُو، فَلَا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِي طَرْفَةَ عَيْنٍ، وَأَصْلِحْ لِي شَأْنِي كُلَّهُ، لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ»
Ma'ana:
"Ya Allah! Rahamarka nake fata. Kada Ka bar ni ga raina ko da ƙiftawar ido ce. Ka gyara mini dukkan al'amurana. Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai."

📚 Abu Dawud ya ruwaito, Al-Albani ya inganta shi.
════🌹════🌹═══

❹ Daga Sa'ad bn Abi Waqqas
(رضي الله عنه),
Annabi ﷺ ya ce:
Addu'ar Annabi Yunus (Dhun-Nun) lokacin da yake cikin cikin kifin ita ce:
«لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظَّالِمِينَ»
Sannan Annabi ﷺ ya ce:
Ma'ana:
"Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Tsarki ya tabbata gare Ka. Lallai ni na kasance cikin masu zaluntar kawunansu."

"Babu wani Musulmi da zai roƙi Allah da wannan addu'a a kan wani al'amari face Allah Ya amsa masa."

📚 Tirmizi ya ruwaito, Al-Albani ya inganta shi.
════🌹════🌹════

🌿 Allah Ya yaye mana dukkan baƙin ciki da damuwa, Ya sauƙaƙa mana al'amuranmu, Ya karɓi addu'o'inmu. Āmīn.

Fassarawa da yaɗawa:
Daga Markazu Amãnil Jãmiy Nigeria
No. 10 Abubakar Kuta Street, by Kwanar Bushara, Makarfi Road, Rigasa, Kaduna, Nigeria.

01/07/2026

SIFOFIN AL-GURABA'U
(Musulman da suke kan abinda Annabi Sallallahu alaihi Wasallama yazo dashi)

Sharhi me kyau ga hadithin
بدأ الإسلام غريبا
Daga Al-Imam Al-Fawzan Hafizahullah
Abubakar Muhammad Salafiyyah a Nigeria - السلفية في نيجيريا Markazu Amãnil Jamiy

30/06/2026

Sharhi me kyau ga hadithin
بدأ الإسلام غريبا
Daga Al-Imam Al-Fawzan Hafizahullah

29/06/2026

Address

Kaduna

Telephone

+2348100327185

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Markazu Amãnil Jamiy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The School

Send a message to Markazu Amãnil Jamiy:

Shortcuts

Share

Category