20/08/2026
INDA BABU ƘASA, AKE GARDAMAR KOKOWA, MAGANA TA KARE!
Wasu daga cikin Gamayyar Matasan Ɗaliban Ilmi na Jihar Sakkwato sun karɓi tayin muƙabalar da Malam Musa Ayuba Lukuwa ya gabatar, domin tattaunawa kan batun da ya shafi alfarmar iyayen shugaban halitta, Annabi Muhammad (S.A.W.).
Yayin da suke cewa ta hannun P.R.O su:
Bayan karɓar wannan gayyata, mun miƙa ma Sheikh Musa Ayuba Lukuwa takardar amincewa da gayyatar da ya yi hannu da hannu, ya kuma karɓa ya saka hannu domin tabbatar da cewa mun amsa wannan ƙalubale cikin girmamawa, tare da niyyar gudanar da tattaunawar cikin tsari, ladabi da mutunta juna.
Haka kuma, mun aika da kwafin takardar zuwa ga hukumomin da abin ya shafa, da kuma ’yan jarida da kafofin yaɗa labarai, ciki har da:
1. Fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi;
2. Hukumar DSS ta Jihar Sakkwato;
3. Rundunar ’Yan Sandan Najeriya;
4. Hukumar NSCDC (Civil Defence);
5. Ofishin Kwamishinan Harkokin Addinai na Jihar Sakkwato;
6. Hukumar Hisbah ta Jihar Sakkwato;
7. ’Yan Jarida da Kafofin Yaɗa Labarai.
Manufarmu ita ce a gudanar da wannan muƙabala cikin ilimi, hujja, natsuwa da mutunta juna, ba tare da zagi, cin mutunci ko wani abu da zai iya haifar da tashin hankali ba.
Mun karɓi gayyatar. Mun aika da amsa. Mun sanar da hukumomin da abin ya shafa, tare da sanar da ’yan jarida da kafofin yaɗa labarai. Yanzu abin da ya rage shi ne a zauna a teburin ilimi, a gabatar da hujjoji, sannan gaskiya ta bayyana.
IN DA BABU ƘASA, AKE GARDAMAR KOKOWA, MAGANA TA KARE!
P.R.O: USMAN ABDULQADIR.
17/08/2026
17/08/2026