Usman Saminu Nuhu

Usman Saminu Nuhu

Share

لله الأمر من قبل ومن بعد

Photos from Usman Saminu Nuhu's post 30/12/2025

Umar M Abubakar
Fatan Alkhairi

Sana TV سنا 15/11/2025

Albishir ga Al'ummar Musulmai.

An fitar da cikakken sautin Tafsirin Alkur'ani da muryar babban Malaminmu Prof. Muhd Sani Umar R/lemo (Hafizahullah)

Malam ne da kansa da muryarsa ya karance tarjamar Tafsirinsa tun daga Fatiha har zuwa Nasi.

Za a iya shiga cikin wannan mahad'ar (Link) domin sauke App na sautin Tafsirin:

https://apps.apple.com/app/id6742054715

Don samun cikakken bayani a leka:

https://sanachannelstv.wuiltweb.com/

Bayin Allah don Allah ku ji wani namijin kokari kuma har wa yau! Babban Malamin ya zauna babu dare babu rana ya rubuta Tafsirin Alkur'ani mafi girma wanda babu kamarsa a yanzu a harshen Hausa, sannan kuma ya sake zama na musamman ya karance tarjamar tsaf domin masu sauraro. Allahu Akbar!

Allah Ya saka wa Malam da alheri, Allah Ya kara masa lafiya da albarka, Ya tsare mana shi.

Mai Rubutu:
Musa Muhammad Dankwano
Sakataren Kwamitin Ilimi na Prof. Muhd Sani Umar R/Lemo

Sana TV سنا

25/10/2025

011. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Mu'ujizozin Manzon Allah صلى الله عليه وسلم :

Allah yana bawa ko wane Manzo Mu'ujiza wadda ta dace da Alummar sa:
1. Annabi Salih Allah ya bashi Taguwa.
2. Annabi Musa an Bashi Sanda ta zama Micijiya.
3. Annabi Isa yana warkar da Makaho, kuturu yana raya Matacce da izininAllah.

Allah ya daukaka Manzon Allah صلى الله عليه وسلم a cikin Annabawa sa Manzannin sa, Allah ya sanya shi mafificin Annabawa shugaban Manzanni, Allah ya bashi wasu Mu'ujizozi wadanda s**a gagari Mutum da Aljani.

- Wasu daga cikin Mu'ujizozin Manzon Allah صلى الله عليه وسلم:
1. Alkur'ani Mai Burma.
2. Isra'i da Mi'iraji.
3. Tsagewar Wata.
4. Magana da Dabbobi da Dutse.
5. Karuwar Abinci da Abin Sha saboda Albarka Manzon Allah صلى الله عليه وسلم.

ALKUR'ANI MAI GIRMA:
Mafi girman mu'ujizar da Allah ya bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم itace Alkur'ani Mai girma, Mu'ujizar da ta gagari Mutum da Aljani, duk yadda Larabawa s**a kai ga iya tsara zance amma kawo kwatankwacin Alkur'ani ya gagari su.
Allah (madaukakin Sarki ) ya kalubalanci Mutum da Aljani su kawo kwatankwacin Alkur'ani yace:
قل لئن اجتمعت الإنس والجن على أن يأتوا بمثل هذا القرءان لا يأتون بمثله ولو كان بعضهم لبعض ظهيرا.
(Ka ce da su: "Wallahi da Mutune da Aljannu sun hadu kan su kawo irin wannan alkur'anin, to ba za su zo da irinsa ba, ko da kuwa wasu sun zamanto suna taimaka wa wasu")

ISRA'I DA MI'IRAJI:
سبحان الذي أسرى بعبده ليلا من المسجد الحرام إلى المسجد الأقصى الذي باركنا حوله لنريه من ءايتنا إنه هو السميع البصير.
(Tsarki ya tabbata ga Wanda ya yi isra'i da Bawansa cikin Dare daga masallaci mai Alfarma zuwa masallaci mafi nisa (na Kudus) Wanda muka albarkaci kewayensa, don mu nuna masa wasu daga ayoyinmu. Lalle shi mai ji ne, mai gani.)

Allah (madaukakin Sarki ) ya bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Wata dama yin isra'i zuwa Masallacin Kudus, sannan daga Masallacin Kudus akayi Sama da shi don ya gana da Allah (madaukakin Sarki ), aka bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Sallah , duk a cikin Dare daya.

MAGANA SA DABBOBI DA DUTSE:

- Allah ya bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم wata Mu'ujiza wadda ya ke Magana da Dabbobi, Wata Rana Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya zo wucewa ta wani Shinge sai ya hangi wani Rakumi ya na cike da damuwa, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya tambaya wannan Rakumin na wane ne sai wani saurayi yace ni ne, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace shin baka ji tsoron Allah akan wannan Dabbar, hakika yawo karar ka cewa kana dara masa kaya masu yawa.

- Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace hakika nasan wani Dutse a Garin Makka yana yimin Sallama kafin a aikoni zuwa Mutane.

KARUWAR ABINCI DA ABIN SHA SABODA ALBARKAR MANZON ALLAH صلى الله عليه وسلم :
- daga Jabir رضي الله عنه yace: mun kasance a Ranar da ake Gina Ramin Gwalalo (Kandak) sai wani falalan Dutse ya bayyana a gare mu mun kasa fasa shi, sai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya mike ya je wajen wannan Dutsen ya dauki Diga ya buga akan wannan Dutsen sai ya fashe, Jabir yace a lokacin naga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya daure cikin sa da Dutse tsawon kwana ba muci Abinci ba, sai na cewa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم a yimin izini zanje Gida, na cewa Matata naga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم cikin wani hali me zamu samu a Gidan sai tace akwai Gãri sai kuma dan Akuya karami Jabir ya yanka shi, akayi Gurasa aka gasa nama, Jabir yace sai naje wajen Manzon Allah صلى الله عليه وسلم na ce akwai Abinci a Gida na zai ishi Mutum Uku zuwa Hudu.
Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace da Sahabban sa kuzo an samu Abinci a Gidan Jabir, Jabir ya shiga Gida ya cewa Matar sa aiki ya same ni Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya kira Sahabban sa duka, tace wa Jabir shin Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya tambaye ka Adadin Abincin yace Eh!.
Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya shiga Gidan Jabir tare da sahabban sa ya fara raba musu wannan Abincin har s**a koshi s**a rage saura, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace ki ci sauran, domin Mutane yunwa ta ci karfinsu.

- Jabir game da abin da ya faru a ranar Hudaybiyyah. Ya ce: "Mutane suna jin ƙishirwa a ranar Hudaybiyyah kuma Manzon yana da tukunyar fata a gabansa. Ya yi alwala, sai mutane s**a yi sauri s**a zo gare shi. Ya ce: 'Me ke damunku?' S**a ce: 'Ba mu da ruwan da za mu yi alwala da shi ko mu sha sai abin da ke gabanka.' Ya sanya hannunsa a cikin tukunyar, sai ruwan ya fara gudana tsakanin yatsunsa kamar maɓuɓɓuga. Mun sha kuma muka yi alwala." Lokacin da aka tambayi Jabir game da adadinsu a wannan ranar, sai ya ce: 'Da mun kasance dubu ɗari, da ya wadatar da mu. Mun kasance ɗari biyar da ɗari biyar.

03/5/1447
25/10/2025

🖋️ Usman Saminu Nuhu


24/10/2025

010. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

النبي أولى بالمؤمنين من أنفسهم وأزواجه أمهاتهم وأولوا الأرحام بعضهم أولى ببعض في كتاب الله من المؤمنين والمهاجرين إلا أن تفعلوا إلى أوليائكم معروفا كان ذلك في الكتاب مسرورا.
(Annabi shi ya fi cancanta ga muminai fiye da kansu; matansa kuma iyayensu ne. Dangi na zumunta kuma shashinsu ya fi kusanci daga wani shashi a cikin Littafin Allah daga kusancin muminai da masu Hijira, sai dai idan za ku aikata wani alheri ne ga masoyanku "muminai". Wannan ya kasance a rubuce a cikin Lauhul Mahafuz)

- Gidan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم:

Manzon Allah a Rayuwar sa a Makka sannan ya auri Nana Khadija a lokacin yana da shekara Ashirin da Biyar (25), Nana Khadija ta na da shekara Ashirin da Takwas (28), ta kasance Matar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ta farko, bai auri Wata Mace ba sai Bayan Rasuwar ta.
Nana Khadija ta haifawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم 'ya'ya Shida (6)
Mazan Sune:

Alkasim da Abdullahi, duka sun Rasu a yarintarsu.

Matan sune:

Zainab, Rukayya, Ummukulsum da Fadima.
1. Zainab ta auri Abil Ãs dan Rabi'a, s**a rabu Bayan ya Musulunta aka Maida auren nasu.
2. Rukayya da Ummukulsum sun auri Usman dan Affan Bayan Rasuwar Rukayya sai aka aura masa Ummukulsum.
3. Fadima ta auri Aliyu bin Abi Dalib Bayan Yakin Badar da Uhud, ta haifi Alhasan, Alhusain, Zainab da Ummukulsum.

- Sauran Matan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم:
Allah ya hallatawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم auren Mata Sama da guda Hudu (4), Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya auri Mata Goma sha Uku, Biyu sun Rasu a Rayuwar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, sannan Biyu Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya rabu dasu kafin su tare, Tara (9) daga ciki sune s**a yiwa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم takaba (Idda).

- Matan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم sha Daya:
1. Khadija yar Kuwailid.
2. Saudat yar zam'a, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shawwal shekara ta Goma da Annabta, bayan Rasuwar Khadija da Wata daya, ta Rasu a Madina a shekara ta Hamsin sa Hudu (54).
3. Aisha yar Abubakar, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shawwal shekara daya da auren Saudat, kafin Hijira da shekara Biyu da Wata Biyar, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya Aure ta Budurwa, ta Rasu a Madina shekara ta Hamsin da Takwas (58).
4. Hafsat yar Umar, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Uku Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Arba'in da Biyar (45).
5. Zainab yar Khuzaima, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Hudu Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Bayan auren ta da Wata Uku.
6. Hindu yar Abi Umayya, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Hudu Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Hamsin da Tara (59).
7. Zainab yar Jahash, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Biyar Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Ashirin (20), ta kasance Matar zaid sai ya saketa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya Aureta.
8. Juwairiyya yar Harisa, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Shida Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Hamsin da Biyar (55).
9. Ramlat yar Abi sultan, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Bakwai Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Arba'in da Hudu (44).
10. Safiyya yar Huyyayi, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Bakwai Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Hamsin da Biyu (52).
11. Maimuna yar Harith, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya aureta a shekara ta Bakwai Bayan Hijira, ta Rasu a Madina Shekara ta Sh*ttin da Uku (63).
- Bayin Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Mata:
1. Mariyatul Kibdiyya, itace ta haifawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Dan sa Ibrahim.
2. Raihana yar Zaid.

02/5/1447
24/10/2025

✒ Usman Saminu Nuhu



23/10/2025

009. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Yaki a Zamanin Manzon Allah صلى الله عليه وسلم:

أذن للذين يقاتلون بأنهم ظلموا وإن الله على نصرهم لقدير.
(Anyi izini "na yin Yaki" ga wadanda ake yaka don ko lalle an zalunce su lalle kuma Allah mai iko ne bisa taimakon su).
Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yayi Hijira da Sahabban sa zuwa Madina, Rayuwa ta canja zuwa mai dadi, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yana yiwa Sahabban sa Tarbiyya tare da koyar dasu Addini.
Allah (madaukakin sarki) ya Umarce su da suyi Yaki don daukaka Addinin Allah, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ne ke jagorantar wannan Yakin, dalilin yin yaki:
1. Daukaka kalmar Tauheed.
2. Daukaka akidar Musulunci.
3. Shigar da Musulunci Garuruwa.

Da jin wannan batun Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Sahabbai رضي الله عنهم s**a fara shirin yin Yaki, har wasu suke tambayar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, akan Mutumin da yayi Yaki saboda Kabilanci, da Wanda yayi Yaki saboda Jarumta, da Wanda yayi Yaki saboda a yabeshi, wanne ne yayi saboda Allah, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace: ( Wanda yayi Yaki daukaka kalmar Allah, shine yayi saboda Allah).

- wasu daga cikin Yakin da Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yayi:

1. Yakin Badar.
2. Yakin Bani Kainuka'a.
3. Yakin Uhud.
4. Yakin Bani Nadeer.
5. Yakin Ahzab/ Gwalalo.
6. Yakin Bani Kuraiza.
7. Yakin Banil Musdalik.
8. Sulhul Hudaibiyya.
9. Yakin Khaibar.
10. Yakin bude Makka.
11. Yakin Hunain.
12. Yakin Tabuka.

01/5/1447
23/10/2025

✒ Usman Saminu Nuhu



22/10/2025

008. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

-Rayuwar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Sahabbai رضي الله عنهم a Madina:

Kafin zuwan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم mutanen Madina sun kasance bass jituwa da juna suna Yakar junan su, lokacin da Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya zo Madina s**a samu Hadin kai, s**a daina Yakar junan su, Allah ( madaukakin Sarki ) ya tabbatar da haka a cikin suratu Ãli-imrana:
واعتصموا بحبل الله جميعا ولا تفرقوا واذكروا نعمت الله عليكم إذ كنتم أعداء فألف بين قلوبكم فأصبحتم بنعمته إخوانا وكنتم على شفا حفرة من النار فأنقذكم منها كذلك يبين الله لكم ءاياته لعلكم تهتدون.
Allah yace: ( kuma ku yi riko da igiyar Allah gaba daya, kada kuma ku rarraba. Kuma ku tuna ni'imar Allah da ya yi musu yayin da kuka zamo 'yanuwan juna a sakamakon ni'imarsa, a da kuma kun kasance a kan gabar Wuta sai ya tserar da ku daga gare ta. Kamar haka ne Allah yake bayyana muku ayoyinsa don ku shiriya).

Zuwan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Madina Wata dama ce ga Musulmai domin Samun yancin yin Ibada cikin Aminci da yin Rayuwa mai yanci, Mawadata da Talakawa kowa yana Rayuwa tare da dan Uwansa.

Yan uwantaka ta hadu tsakanin mutanen Madina da wadanda s**ayi Hijira zuwa Madina, har Mutumin Madina zai cewa dan Uwansa Wanda yayi Hijira ya zabi daya daga cikin Matansa sai ya saketa shi ya Aure ta, haka ma a cikin Kasuwanci, Rayuwa tayi dadi ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Sahabban sa رضي الله عنهم , sannan Mutanen Madina s**a samu yanuwa.

Madina ta zama Daular Musulunci ta farko.

Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya cigaba da karbar wahayi daga Allah (madaukakin Sarki ) na hukunce- hukuncen Musulunci Kamar Alwala, Sallah, Azumi, Zakka, Hajji, Aura, Saki da Kasuwanci dss.

30/4/1447
22/10/2025

✒ Usman Saminu Nuhu



21/10/2025

007. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Hijirar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم zuwa Madina:
Bayan Sahabbai sunyi Hijira zama cewa Musulmai sun bar Garin Makka , sai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya shirya yin Hijira, daga Nana Aisha tace bayacikin dabi'ar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم zuwa Gidan Abubakar رضي الله عنه da Rana sai dai lokacin Safiya ko Yammaci, Amma da aka bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم umarnin yayi Hijira, Manzon Allah صلىالله عليه وسلم ya zo Gidan Abubakar رضي الله عنه sa Rana ba Kamar yadda yasaba zuwa ba, lokacin da Abubakar رضي الله عنه yaga Manzon Allah irin wannan lokacin sai da dalili, Nana Aisha tace Manzon Allah صلى ألله عليه وسلم ya zo Gidan mu, Abubakar رضي الله عنه ya sauka daga kan abun zaman sa yabawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya sauna, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya cewa Abubakar رضي الله عنه anyi min umarni inyi Hijira sai Abubakar yace in zama Abokin Tafiyar ka, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace eh!, Nana Aisha tace Abubakar رضي الله عنه saboda farin ciki har saida yayi kuka, sai Abubakar رضي الله عنه yace ga wasu Rakuma Biyu domin wannan Tafiyar.
Nana Aisha tace muka shirya musu kayan Tafiya, Asma'u ta yaga mayafinta Biyu ta daura kayan nasu, sai ManzonAllah صلى الله عليه وسلم da Abubakar رضي الله عنه s**a fita ta kofar baya s**a isa zuwa Kogo cikin Dutsen Thaur, s**a Boye tsahon kwana Uku.
Abdullahi dan Abubakar a lokacin yaro ne mai fikira ya wayi gari a Makka yana jin mai Mushrikan Makka ke tsarawa aka Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, da yamma ya zo ya sanarwa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Abubakar رضي الله عنه halin da ake ciki, shi kuma Ãmir dan Fuhaira bawa ne ga Abubakar رضي ألله عليه وسلم ya na kiwon Dabbobin Abubakar رضي الله عنه sai ya matsar da Dabbobin kusa da Kogon lokacin Isha'i Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Abubakar رضي الله عنه su tatsi Nono haka yadinga yi tsahon kwana Uku.
Suna cikin Kogo a wannan Kwanakin yan farautar Kuraishawa suna yawon neman Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Abubakar رضي الله عنه Amma basu same suba s**a zo kusa da Kogon har Abubakar رضي الله عنه yake cewa da dayansu zai duba kafar sa zai ganmu, sai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace menene zatonka Mutum Biyu Allah ne na Ukun su, Allah yace cikin Suratut-Tauba:
إلا تنصروه فقد نصره الله إذ أخرجه الذين كفروا ثاني اثنين إذ هما في الغار إذ يقول لصاحبه لا تحزن إن الله معنا....

- Isowar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Madina:

Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya fita daga Kogo bayan Kwana uku ya nufi hanyar Madina.
Lakacin da Musulmai a Garin Madina s**a ji labarin futowar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم zuwa Madina, suna fitowa kowace Rana su zo wajen Gari don jiran karasowar Manzon Allan صلى الله عليه وسلم su fito tun safe har yamma, Wata Rana sun fito zafin Rana ya maida su Gidajen su, sai wani Mutum ya hau Saman Gidan sa sai ya hangi Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Abokin Tafiyar sa ( Abubakar), Mutumin yayi Kira da Muryar sa cewa ya Larabawa Wanda kuke tsumayi ya zo sai Musulmai s**a dinga fitowa domin tarar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم a tsakiyar zafin Rana, ya sauka a kabilar Bani Amru dan Auf a Kuba'a, A Ranar Litinin Watan Rabi'il auwali.

29/4/1447
21/10/2026

✒ Usman Saminu Nuhu


20/10/2025

006. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Hijira zuwa Garin Yathriba (Madina):
Lokacin da Mutanen yathriba s**ayi mubayi'a ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم tare dayin biyayya ga Abunda Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya zo dashi, s**ayi Alkawarin kare Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da dukkanin Karfinsu.

- Dalilan yin Hijira:
1. Tabbatar da Daular Musulunci.
2. Jihadi don daukaka Addinin Allah.
3. Yin Ibada cikin Aminci.
Yin Hijira isharace Allah (Madaukakin Sarki) yayi wa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Kamar yadda Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya gani a cikin Mafarkin sa cewa: an nuna min nayi Hijira zuwa Gari dayake da Dabinai, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace natsammaci Garin Yamama ko Garin ----- Hajar ashe Garin Yathriba me.
Sai Sahabbai رضي الله عنهم s**a fara shirin tafiya, suna fita a Boye, Mutum na farko daya fara zuwa Madina Abu salamat bin Abdulasad sai Ãmir bin Rabi'a da matar sa Laila bint Abu Haithma itace Mace ta farkon zuwa Madina.
Yayin da suna tayin Hijira Mushrikan Kurashawa nata Azabtar da wadanda basu da galihu, wadanda s**ayi Hijira s**a zauna a Kuba'a inda Sãlim Maula Abi Khizaifa yake yi musu Sallah kafin zuwan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yazo Madina.
Garin Makka ya zama Babu Wanda s**ayi saura sai:
1 - Manzon Allah صلى الله عليه وسلم.
2 - Abubakar.
3 - Aliyu.
4 - sai wadanda aka fitina, Marasa Lafiya da Masara galihu.

Mushrikan Kuraishawa s**a samu Wata hanya don kuntatawa Musulmai:
1. Rabatsakanin Ma'aurata, miji da Mata da 'ya'ya.
2. Kwace Dukiyar Musulmai.
3. Tsarewa.
4. Azabtarwa.

- Taron Kuraishawa a Gidan shawara:
Yayinda Kuraishawa s**a ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya samu mabiya a wani Gari da ba nasuba, s**a ga Sahabbai رضي الله عنهم sunyi Hijira sun Sami wajen zama mai Aminci, s**a ji tsoron fitar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, sai s**a shirya taro a Gidan shawara ( Gidan Kaisy bin Kilãb) s**ayi shawara yaya za suyi da Manzon Allah صلى الله عليه وسلم , bayan sun tattauna sai s**a tabbatar da Kisan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم s**a zabi Matasa daga kowace Kabila daga Kabilun Makka.
Allah ya saukar wa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم labarin Abunda s**a aikatam Allah yace:
وإذ يمكر بك الذين كفروا ليثبتوك أو يقتلوك أو يخرجوك، ويمكرون ويمكر الله والله خير الماكرين.

8/4/1447
20/10/2026

✒ Usman Saminu Nuhu


19/10/2025

005. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Bujirar da Addinin Allah ga Kabilu :

Bayan Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya dawo daga Da'if ya fara gabatar da kansa ga Kabilun Larabawa a taruka, yana kiran su zuwa Addini Allah, a cikin wannan hali sai Wata tawagar Mutum Shida (6) daga Yathriba (Madina ) s**a zo wajen Manzon Allah صلى ألله عليه وسلم, Bayan zuwan su ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Shekarar Hajji ta so sai Wata tawagar Mutum Goma sha Biyu (12), Goma daga Khazraj, Biyu daga Aus (2) s**ayi mubayi'a ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, Ubadata dan Samit رضي الله عنه yace mubayi mubayi'a ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم akan ba zamu karshe 'ya'yan mu ba, lokacin da zasu koma Yathriba (Madina) Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya Shugabantar musu da Mus'ab dan Umair رضي الله عنه, a shekara ta Goma sha uku (13) da Annabta lokacin Hajji ya zo sai Adadi mai yawa daya kai Saba'in (70) na Musulman Yathriba ( Madina) s**a zo ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم s**ayi Mubayi'a ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم.

- Shuwagabani daga Kabilun Yathriba (Madina) :

1. Khazraj:
- As'ad dan Zurãra.
- Sa'ad dan Rabi'I.
- Abdullahi dan Rawãha, dss.
2. Aus:
- Usaid dan Khudair.
- Sa'ad dan Khaithama.
- Rufa'a dan Abdulmunzir

27/4/1447
19/10/2026

✒ Usman Saminu Nuhu


18/10/2025

004. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Shekarar Bakin ciki:
A shekara ta Goma (10) da Annabta Abu Dalib ya Rasu, ya kasance yana bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم kariya daga cutarwar Kuraishawa, bayan Rasuwar Abu Dalib Sayyada Khadija ta Rasu, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya shigacikin damuwa domin masu bashi kariya da gudunmawa sun bar Duniya, wannan shine dalilin sanyawa wannan shekara da Shekarar Bakin ciki, Bryan Rasuwar Abu Dalib sai Kuraishawa s**a tsanta Cutarwa ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم.

- Tafiyar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم zuwa Da'if:
Cutarwar Kuraishawa ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم bayan Rasuwa Abu Dalib sai ya tafi zuwa Da'if don kiran su zuwa Addinin Allah da kuma neman Agajin su da taimakon su, Amma sai s**a kore shi s**a turo mutanen su da Wawayen su s**a dinga jifan manzon Allah صلى الله عليه وسلم har Jini na zuba a Kafafuwan sa صلى الله عليه وسلم, manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya dawo cikin Bakin ciki.

- Isra'i da Mi'Iraqi
Shekara Daya kafin Hijira zuwa Madina akayi isra'i da Manzon Allah صلى الله عليه وسلم da Jikinsu daga Masallachi Mai Alfarma zuwa Baitul Mukaddas, ya hau Taguwa (Buraka) tare da Mala'ka Jibril yayi Raka'a Biyu Acikin Masallachi Kudus.
Sai s**a nufi Sama tare da mala'ika Jibril, s**a haura matakai na Sama har zuwa Sidratul-Muntaha sai aka daukaka Manzon Allah صلى الله عليه وسلم zuwa ga Allah ( Madaukakin Sarki) aka bawa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم Salloli Hamsin (50) bayan ya taho sunyi Muhawara da Annabi Musa, ya koma ga Ubangiji ( Madaukakin Sarki) aka maida Sallah ta zama Sallali Biyar (5) aka tabbatar da Salloli Biyar.
سبحن الذي أسرى بعبده ليلا من المسجد الحرام إلى المسجد الأقصا الذي بركنا حوله لنريه من ءايتنا إنه هو السميع البصير

26/4/1447
18/10/2026

✒ Usman Saminu Nuhu

17/10/2025

003. Annabir-Rahama صلى الله عليه وسلم

Da Sunan Allah mai Rahama Mai Jinkai, tsira da amincin Allah s**ara tabbata ga Annabi Muhammad dan Abdullahi.

- Hijirar Musulmai zuwa Habasha:

Lokacin da tsananin Cutarwa ga Musulmai ya yawaita sai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya tura wasu daga cikin Musulmai zuwa (Habasha) a lokacin da Allah ya saukar da Aya a Suratuz-zumar da tayi nuni ga yin Hijira in da Allah (madaukakin Sarki) yace:
قل يا عباد الذين ءامنوا اتقوا ربكم للذين أحسنوا في هذه الدنيا حسن وأرض الله واسعة وإنما يوفى الصابرون أجرهم بغير حساب
Manzon Allah yace a Habasha akwai Sarki Adali ( Najjashi), Musulmai s**a doshi Kasar Habasha Kuraishawa s**a bi sahunsu amma basu samesu ba bayaMusulmai Sun isa Kasar Habasha Sun Sami kyakyawar tarba, bayan wani lokaci Musulman da s**ayi Hijira labari ya ishe su cewa wai Kuraishawa sun Musulunta wannan rade - radin shine dalilin dawowar su, sai Kuraishawa s**a cigaba da Azabtar da Musulmai. Sai Musulmai s**a sake komawa Habasha a karo na Biyu Wanda adadin su Maza Tamanin da uku (83) da Mata Goma sha Tara (19).
Sai Kuraishawa s**a tura wakilai zuwa ga Sarkin Habasha (Najjashi) a cikin su akwai. Amru dan Ãs da Abdullahi bin Abi Rabi'a domin su dawo sa Musulmai s**a tanadi Kyaututuka domin subawa sarkin Habasha da Fadawan sa don ya basu Musulman da s**a je Habasha, Sarki Najjashi yace bazan baku su ba har sai naji dalilin su .
Najjashi yasa aka kira Musulmai a karkashin Ja'afar bin Abu Dalib رضي الله عنه, Najjashi ya tambayi Ja'afar dalilin zuwa su Kasar (Habasha) sa, sai Ja'afar yace: ya Sarki min kasanece a cikin Wata Alumma muna bautar Gunki, Zalinci, Cin Mushe, Alfasha da yanke Zumunci muna cikin wannan halin sai Allah (madaukakin Sarki) ya turo mana Manzo mun san Asalin sa da Amanar sa ya Umarce mu da my Bautawa Allah shi kada, ya hane mu da Cin Amana, Zalinci, Karya da Alfasha, dss.
Ya Umarce mu da yi Sallah, Zakka da Azumi, Ja'afar ya lissafa abubuwa da dama wanda Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya zo dasu sai Najjashi yace shin akwai wani Abu cikin Abunda Manzo ya zo dashi, sai Ja'afar ya Karanta masa farkon suratu Maryam har sai da Hawaye s**a Jika Gemun Sarki ( Najjashi ) Ayn fadar sa s**a zubar da Hawaye, sai Najjashi yace na rantse sa Allah wannan sakon irin sakon da Annabi Musa ya zo dashi ne yace Wallahi bazan Baku su ba sai Najjashi ya kori wakilan Kuraishawa.
Najjashi ya Musulunta kuma yayi Imani da Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya Mutu a Musulunci.

-Dalilan yin Hijira:

1. Tsira da Addini.
2. Kira zuwa Addini Allah.
3. Samun wajen yin Ibada cikin Aminci.

25/4/1447
17/10/2026

✒ Usman Saminu Nuhu


Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Telephone

Address

Kano