Malam Shehu Mansur Dala

Malam Shehu Mansur Dala

Share

Shafi ne da aka samar da shi domin fadakarwa akan addini da rayuwa.

18/08/2026

Ba kowa ke nufin ka da sharri ba❗

16/08/2026
14/08/2026

Hudubar juma'a

Me taken
Girman Alwala da muhimmancin ta a Musulunci...

Mal. Alkasim Yusif (Hafizahullah)

Masjid Abdullahi Bin Umar, Bakariyya Group of schools, Turba waika waje, Kano.

Juma'a
1/03/1448==14/08/2026

14/08/2026

JAN HANKALI TUN KAFIN DAMA TA WUCE

Da dama daga cikin iyayen mu da kakannin mu da yan uwansu,da yayyen mu da kannenmu ,da yayansu,da Malaman mu,da abokan mu,s**an mutu ba su mori wani abin a zo a gani ba daga arziki da dama da Allah ya ba mu a rayuwa.

Hakan na faruwa ne saboda mafi yawancin mu ba ma yi wa wadanda suke da tasiri a rayuwar mu wani gagarumin alhairi wanda zai taba rayuwar su kai tsaye, har sai sun roke mu,ko kuma sai mun ga sun shiga wani mawuyacin hali na dab da mutuwa,su kuma ba su iya roko ba, wani da ya roki dan sa na cikin sa ma gara ya kwana da yunwa ,ballantana ya roki dalibinsa ko dan dan uwansa ko abokinsa ,kuma ba dukkanninsu ne Allah yake jarrabar su da shiga wani halin innalillahi ba ,ballantana a kwashe su a kai su asibiti ko a watsa musu ruwan kashe gobara .
Mu kuma muna kallon su haka za mu bar su saboda ba mu da sanin ya kamata.

Cikar mutuncin mutum shi ne ya taimaki wanda ya cancanci taimakonsa da abin da ya kamata a lokacin da ya kamata ba tare da ya yi yar murya ba , ba tare da ya zata ba kawai ya ji dumus a yi masa abin da ba zai taba mancewa da shi ba,abin da kai kan ka za ka san ka yi abin da ya dace.

Shin za ka yi abin da ya dace ga wanda ya dace tun yanzu ko za ka bari sai ya kai lokacin da ba zai mori abin da ka yi masa ba,ko kuwa sai ya mutu ka zo kana surutai marasa amafani ?

Lallai ya zama wajibi mu yi amfani da damar mu tun kafin damar ta wuce...

Shehu Mansur Dala
26/3/1446
30/9/2024

13/08/2026

Daura me taken hadisai arba'in

Mako na biyu
Hadisai Arba'in kan illollin lalata, (zina madigo da lalata).

13/08/2026

SARKIN KAMSHI,MANZON ALLAH SALLAHU ALAIHI WASALLAM.

Allah Taala ya cika dukkanin niimominsa da darajoji da baye baye ga babban bawansa masoyinsa shugaban halitta gaba daya sallahu alaihi Wasallam,,kuma ya kebance shi da waɗansu darajojin da a cikin dukkanin halittu shi kadai ya yiwa wannan gatan.

Duk bangaren da ka duba In dai abu ne da ya shafi girma da daukaka da mutunci da kamala da martaba da isa za ka ga Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya fi kowa.Babu wani mahaluki da za a kwatanta shi da shi ya yi kusa da matsayinsa ko su yi daidai ballantana a ce ya zarta shi, wannan mahaluki Malaika ne ,ko Aljan ne ko mutum ne.Ba a yi kamarsa ba ,kuma ba za a sake yin kamarsa ba.

A cikin darajoji da niimomin da Allah Taala ya yi wa manzonsa Sallallahu alaihi Wasallam akwai cikakken tsarki da tsafta da kanshi a lokacin da yake raye da kuma lokacin da ya koma ga mahaliccinsa.
Wannnan abu ne da babu wani ja in ja a kansa a tsakanin dukkannin musulmi masu ilimi da imani ,kuma ba wata mas'ala ce da ake tattaunawa a kanta ba don wai a tabbatar haka ne ko ba haka ba ne, a'a,sai dai don a kara tabbatar da gaskiyar ta,da kuma neman albarkacin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam da tunawa juna martabobinsa da darajarsa, sallahu alaihi Wasallam.

_An karbo daga Jabir dan Samurata Radiyallahu anhu ya ce:"Na yi sallar Azahar tare da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam,sai ya koma gida,na tafi tare da shi,sai yara s**a tare shi,sai ya rinka shafa fuskarsu daya bayan daya.Ni ma ya shafa fuska ta sai na ji wani sanyi ko kanshi a hannunsa kamar daga kwandon mai sayar da turare ya ciro hannun nasa'.(Muslim 2329)

_An karbo daga Anas ɗan Malik Radiyallahu anhu ya ce :"Tunda nake ban taba shaƙar wani turaren Ambar ko Miski ko wani abu mai kamshi ba,irin kamnshin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam.Kuma ban taba taba wani abu mai laushi ba koda alhariri ne wanda ya fi hannun Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam taushi ba'(Bukhari 3561,Muslim 2330)

A nan akwai wata darajar bayan kamnshin, wato kyawun jikinsa da laushin fatarsa tare da cewa ya fi kowa jarumta kuma yana baya baya da duniya ba ya holewa irin ta yan duniya, amma a maimakon a samu kaushi ko yaushi a fatarsa sai Allah ya inganta masa ita ta zama irin ta masu jin daɗin duniya, Sallallahu alaihi Wasallam.

_An karbo daga Anas ɗan Malik Radiyallahu anhu ya ce :"Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya shigo gidanmu ya yi barcin rana,sai ya yi gumi,sai baba ta ta samu kwalaba tana tarar gumin a ciki.Sai annabi sallahu alaihi Wasallam ya farka ,sai ya ce :" Me k**e yi haka Ummusulaim ?Sai ta ce wannan gumin naka muna sanya shi ne a cikin turaren mu,sai ya zama ya fi kowane turare kamshi'(Bukhari 6281 Muslim 2332)

_An karbo daga Anas ɗan Malik Radiyallahu anhu yace :Idan manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya bi ta hanya sai a yi ta jin kamnshin almiski a hanyar,ta haka ake gane cewa ya bi hanyar'(Bazzar da Abu Yaala ne s**a ruwaito shi da isnadi mai kyau/Sharhusshifa na Aliyul Kari 1/167)

_Ishak Ibn Rahawaihi Rahimahullahu ya ce : "Wannan kamshin nasa haka yake ko bai sa turare ba, sallahu alaihi Wasallam'(Asshifa1/64)
Wannan a lokacin rayuwarsa ke nan ,Sallallahu alaihi Wasallam,to bayan wafatinsa ma haka abin yake.

_An karbo daga Uwar Muminai A'ishah Radiyallahu anha a cikin hadisin da ta ba da labarin wafatin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ta ce"Sai Abubakar ya zo ,sai ya bude fuskar manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam,sai ya sumbance shi sai ya ce:Iyaye na su zama fansa a gare ka ,ka yi kamshi kana raye ,ka yi kamshi bayan ka yi wafati.Na rantse da wanda rai na yake hannunsa Allah ba zai dandana maka mutuwa biyu ba'(Bukhari 3667 da malaman hadisi da dama)

_An karbo daga Sayyidina Ali Radiyallahu anhu ya ce:"A lokacin da na yi wa manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam wanka sai na rinka dubawa ko zan ga ga irin abinda aka saba gani a jikin gawa,ban ga komai ba,ya kasance mai kamshi a lokacin da yake da rai da lokacin da ya yi wafati.
A wani lafazin ya ce : Uba na ya zama fansa a gare ka tsarkakakke.Ka kamsasa kana da rai,ka kamsasa bayan ka yi wafati'
(Ibn Majah 1467,Hakim 1339,Baihaki 6865.) Hadisi ne ingantacce.

_An karbo daga Uwar Muminai A'ishah Radiyallahu anha ta ce : "An karbi ran manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam a hannu na yana tsakanin haba ta ta da kirji na.Ta ce : Da ran sa ya fita sai na ji wani kamshi da ban taba jin irinsa ba'(Musnad Ahmad 24786) Isnadinsa ingantacce ne.

_Ibn Abubakar ya ruwaito a cikin littafinsa na Sira cewa:Uwar Muminai Ummusalama Radiyallahu anha ta ɗora hannunta a kan kirjin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam bayan ya yi wafati ,sai da ta yi satuka masu yawa tana jin kamshin almiski a duk lokacin da ta zo cin abinci ko ta zo yin Alola.(Sharhusshifa na Aliyul Kadi 1/167)

Wannan shi ne abinda ya tabbata kuma babu wani musulmi mai imani da ilimi da yake da wani shakku akan haka.

SHUBUHOHI

Sai dai kuma akwai wasu shubuhohi da waɗansu kiristoci da mufukai da kuma masu daka ta tasu suke ta yadawa akan wannan magana ,su Kiristoci da mufukai suna yi ne domin cin zarafin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam, sannan kuma su tayar da hankalin musulmi su girgiza imaninsu. Su kuma masu daka ta tasu a cikin musulmi masu da'awar ilimi da da'awar kare martabar manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam,suna yada shubuhar ne don su ci zarafin Sahabbai da manyan malaman musulunci,sannan kuma wai don kare martabatabar manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam.

Wannan shubuha ita ce waɗansu maganganu raunana da aka ruwaito su daga Hasanul Basari,da Ikrima daga Abbas dan Abdulmutallib,da Zuhri daga Anas ɗan Malik Radiyallahu anhum.

Wadannan raunanan maganganun suna nuna cewa jikin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya canja kafin a binne shi.
Wadannan ruwayoyi ba su inganta ba ,kuma bai halatta ga duk wani musulmi mai imani da ilimi ba mai kaunar manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam da ganin girmansa ya rinƙa yada wadannan maganganu sai dai In da nufin bayanin matsayinsu da rauni su da hatsarinsu,saboda wadannan dalilai :

1.Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ya ce:"Hakika Allah ya haramtawa kasa cin naman Annabawa' Hadisi ne ingantacce Ahmad 16162,Abudawud 1047,Nasai.1374 daga Aus dan Aus Radiyallahu anhu.

2.Babu wani sabani tsakanin malamai akan tsarki da kamshin jikin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam a lokacin da yake da rai da bayan wafatinsa.

3.Raunin wadancan ruwayoyi da suke nuna sabanin haka
_Maganar Hasanul Basari Ibn Sa'ad ya ruwaito ta a Tabakatul kubra 2/271 da rarraunan isnadi ,saboda Hasanul Basari Tabii ne ,bai fadi a wurin sababin da ya ji hadisin ba,wato hadisi ne Mursali.Kuma irin wadannan Marasil na Hasanul Basari sune mafiya raunin mursalai.
Sannan kuma Ibn Adiyyin ya ruwaito shi a Kaamil 7/48,da Ibn Asakir a Tarikh Dimashqa 63/100 ta hanyar Wakiu da Abdullahi Albahhi.
Wannan ma bai inganta ba saboda shi Bahhi Tabbii ne kuma an yi sabani akan matsayin sa ,sannan kuma hadisi ne Munkari ya ci karo da ingantattun hadisai.

Shi kansa Wakiu ya ci duka a hannun mutane ta yadda da kyar ya sha a lokacin da tsautsayi ya sa shi ya fadi wannan hadisin.Imam Zahabi ya ce: Wannan wata zamiya ce ta malamai ,me ya kai Wakiu fadar wannan mummunan hadisi rarrauna ?(Siyarul aalam :7/570)

_Ita ma ruwayar Ikrima daga Abbas Radiyallahu anhu ba ta inganta ba,ruwaya ce mai rauni(Munkadia) saboda Ikrima bai riski Abbas ba.
Ita kuwa ruwayar Ibn Shihab daga Anas ɗan Malik Radiyallahu anhu sam babu maganar halin tsarkakken jiki na manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam a cikinta.A duba Dabakat na Ibn Sa'ad 2/266

Amma kuma saboda tsananin kiyayya ga Anas da Ibn Shihab Azzuhri wadansu suke ta zabinsu wai saboda sun fadi wannan magana,alhali ba su fada ba..
Kuma koda.a ce ta inganta ai ra'ayi ne da fahimta ta Abbas Radiyallahu anhu kuma ta ci karo da hadisai ingantattu.

Shaihin Malami Abdulaziz Ibn Baz Rahimahullahu ya fada a fatawar sa 26/107 :Amma maganar Abbas Ni har yanzu ban san ingancin ta ba,kuma ban bibiyi isnadinta ba'
Wannan itace tatacciyar magana ingantacciya wacce duk wani musulmi mai imani da ilimi da ganin girman Manzo Allah Sallallahu alaihi Wasallam da ba shi kariya ta gaskiya yake kan ta.

Daga karshe ina kira ga yan'uwa na dalibai da su guji gaggawar karyata wani hadisi ko wata magana ba tare da wani zuzzurfan bincike ba,haka kuma su guji gayawa Sahabbai da bayin Allah managarta maganganu munana da ƙaryata su da cin mutuncinsu saboda waɗansu shubuhohi da makiya musulunci suke yadawa ba tare da sun koma ga bayanan malamamai ba akan wadannan shubuhohin.

Ya kamata kowa ya sani cewa duk wata shubuha ko rikici da rudu da za a zo da su daga ɓangaren kafirai ko munafukai ko jahilai ko wasu rudaddu akan komai na musulunci,tuni malamai sun yi bayani mai warkarwa akan su,bincike kawai za yi a karanta ,amma ƙaryata sahihan hadisai da cin mutuncin Sahabbai da bayin Allah managarta ba hanya ce ta ilimi ba,ba kuma hanya ce ta masu imani ba,hanya ce mai hatsari wacce za ta iya raba mutum da musulimci baki daya ,kuma ba ta wannan hanyar ake ba da kariya ga martabar Musulunci da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam ba.
Kuma ba iyar shubuhohi da yada su da barin ayoyi da sahihan hadisai da kyawawan maganganu na malamai na kwarai ,dabi'a ce ta munafukai da kafirai da wadanda imaninsu yake da rauni da wani kaikayi ,sune wadanda Allah Taala ya siffanta su daالذين في قلوبهم زيغ a cikin Suratu Al Imran aya ta bakwai.
Sai su kau da kan su daga ayoyi da hadisai bayyanannu,kuma su kangarewa gamsasshen bayanai da s**a.dace da shin ilmi da lafiyayyen hankali,su yi ta zakulo rubabbun maganganunsu rudani iri iri suna yadawa suna ƙaryata tabbatattun al'amurra na musulumci.

Allah ka ganar da mu gaskiya ,ka ba mu ilimi mai amfani ka tsare imaninmu,ka ba mu lafiya da zama lafiya ,ka faranta mana duniya da lahira.

Shehu Mansur
24/12/1441_13/8/2020.

12/08/2026

Karatun Littafin

طريق الصالحين إلى رب العالمين

Darasi na 8

Falalar sallah a masallaci

Tare Malam Shehu Mansur Dala
Daga Masjid Ibrahim Bulbula Koki

Want your school to be the top-listed School/college in Kano?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Address

Turba Waika Waje
Kano