16/02/2024
Insha Allahu a wananan takarar tamu Idan Allah ya bamu Nasara zamu fi mayar da hankali akan Muhimman Abubuwa guda 3.
1) Harkar Ilimi
2) Harkar gyaran Unguwa
3) Taimakawa Masu neman taimako.
1) Harkar Ilimi :- A wananan Mazaba tamu Insha Allahu zamu kawo Karshen adadin Yara Maza da mata mara sa zuwa makaranta, zamu taimaka musu da Uniform da littattafai da sauran kayan karatu. Za kuma mu nemar Wa Masu Primary qualification da admission zuwa Secondary school, da Masu Secondary zamu nema musu Jamb domin suma su tafi zuwa University ko College.
Bangaren karatun Addini muna da makarantu da suke fama da matsalar wuraren karatu, insha Allahu zamu kai matsalar su gaban Chairman na L.G. Zamu kawo Karshen matsalar tabarmin zama a makarantun mu na Allo dana Islamiyya, Sananan Masu bukatar haske zamu kawo musu wananan tallafin, za kuma mu shigar da Malamai wannan bangaren domin shawarwari Akan yadda za a kawo Karshen matsalar Insha Allahu. Domin Ilimi shine mabudin duk wani Alheri. Jahilchi kuwa shine mafarin duk wata Futina.
2) Harkar gyaran Unguwa :- A Zaitawa yankin mu na Yan Awaki da sauran wasu Yankunan yana fama da matsalar magudanan ruwa inda ake yawan samun matsala lokachin damuna, ruwa yana shigarwa mutane har cikin gidajen su, Insha Allahu zamu samar da tsarin share muhalli duk Karshen wata ko kuma lokachi zuwa lokachi, Sannan zamu samar da kayan Aikin na dindin din a kowane yanki na Zaitawa Ward.
3) Taimakawa Masu neman taimako :- Muna da mutane Masu neman Taimako Akan rayuwar su ko kuma wata matsala da take damun su, ko rashin lafiya ko wata matsalar ta rayuwa.
Muna da Mata Masu neman Jari, Insha Allahu zami empowerment na Maza da Mata domin ragewa Mutanen mu radadin rayuwa. Sannan duk sanda Muka Sami labarin Empowerment ko wani Abu Wanda Gwamnatin Local ko State government zata yi zamu nemar Wa Mutanen mu Insha Allahu.
Insha Allahu Idan Allah ya bamu Nasara zami Abubuwan da s**a fi haka, za kuma mu tafi da matasa Yan uwan mu Maza da Mata.
All