Hausa Rumbun Hikima

Hausa Rumbun Hikima

Share

Is All About Enlighten People And Reminding Them On Something They Knew but Forget or Don’t

05/06/2026

Murmushin Tsakanin Duniya Biyu: Labarin Soyayyar Rasulullah ﷺ da Fatimah az-Zahra رضي الله عنها

Lokacin da Rasulullah ﷺ yake kan gadon mutuwa, Fatimah رضي الله عنها ta shigo cikin ɗakin.

Sai ﷺ yayi mata wasu maganganu a kunne.

Ta fashe da kuka.

Sai ya sake yi mata wasu maganganu a kunne.

Ba zato ba tsammani, fuskarta ta haskaka da murmushi.

Daga baya, Aisha رضي الله عنها ta tambaye ta, “Me ya ce Maki?”

Fatimah ta amsa:
“Da farko, ya gaya mini cewa yana gab da mutuwa, don haka na yi kuka. Sai ya gaya mini cewa zan zama na farko daga cikin iyalansa da zai hadu da shi. Saboda haka na yi murmushi.”
(Sahih al-Bukhari 3624)

Bayan da Annabi ﷺ ya bar duniya, Fatima az-Zahra — wadda take haskakawa — ta dushe.

Ta kasance tana cewa sau da yawa:
“Babu wani bala’i da ya taɓa samu na fiye da mutuwarka, ya Rasulullah ﷺ.”

Ta yi kuka har mutanen Madina s**a ce mata:
“Ya ’yar Rasulullah, kukan ki yana damun mu.”

Baƙin cikinta ya kasance k**ar tsaunuka.

Bayan watanni shida kawai, Fatimah ta yi rashin lafiya. Ta san lokacinta ya kare.

Ta faɗi a hankali wa kuyanginta:
“Ki zuba mini ruwa in yi wanka. Ki lulluɓe ni da sabbin tufafina kuma ki ajiye ni inu fuskantar Qibla.”

Sai ta kwanta, ta rufe idanunta, kuma ta jira — tana tunawa da maganar mahaifinta: “Zaki zama ta farko wanda zata hadu da ni.”

Ali ibn Abi Talib رضي الله عنه ya shigo ya same ta tana murmushi a cikin mutuwa.

Ba murmushin zafi da ke barin jiki ba ne.

Murmushin ’yar da ta sake ganin ƙaunataccen mahaifinta ne.

A hannunta akwai wani yanki na rigar Annabi wanda ta ajiye kusa da ita tun bayan an binne shi. Ta riƙe shi yayin da take komawa gare shi.

Tana da shekara 29 kawai.

Ta bar ’ya’yanta — Hasan, Husayn, Zaynab, da Umm Kulthum رضي الله عنهم — da kuma al’ummar Musulmai masu baƙin ciki.

Amma ta samu abin da zuciyarta ta fi so: mahaifinta ﷺ.

Watanni shida na rabuwa sunyi k**ar dawwama ga irin zuciyarta.

Wannan soyayya ce da ko mutuwa ba za ta iya karyawa ba.

Mahaifi wanda ya ta’aziyar ’yarsa a kan gadon mutuwarsa.
’Yar da baƙin cikinta ya zama ibada, kuma murmushinta a mutuwa ya zama tabbataccen imani.

Alaƙarsu ta kasance na duniya da Lahira.

Wannan shine abin da “iyali” ke nufi a Aljanna.

Ga kowace ’ya mace da ke kewar mahaifinta…
Ga kowane uba da ya binne ƙaramar ’yarsa…

Ba ku kasance ku kaɗai ba.

Haɗuwa ta gaskiya ce.
Murmushi yana zuwa.

> “Kuma waɗanda s**a yi imani kuma zuriyarsu s**a bi su da imani — Za Mu haɗa su da zuriyarsu…”
> (Surah At-Tur 52:21)

Sahih al-Bukhari, Ibn Sa’d’s
Tabaqat, Sahih Seerah.

~👨🏾‍💻✍🏾📝

05/06/2026

Labarin Mutumin Da Ya Guduwar Ma Mutuwa Zuwa Kasar Indiya

​A lokacin Annabi Sulaiman (Alayhis Salam), akwai wani mutum da yake zaune a cikin fada (majalissa) ta Annabi Sulaiman (A.S).

​Wata rana, sai wani mutum daban ya shiga cikin fadar.

Wannan mutumin kuwa ba kowa ba ne face Mala'ikan Mutuwa (Malakul Maut), wanda ya bayyana a surar dan Adam.

​Haka kawai yana shiga, sai ya fara zura wa wani matashi da ke zaune kusa da Annabi Sulaiman (A.S) idanu cikin tsananin duba.

Mala'ikan Mutuwa ya rika kallonsa akai-akai, har sai da wannan matashi ya cika da tsoro da fargaba.

Bayan dan lokaci kadan, sai Mala'ikan Mutuwa ya fita ya bar fadar.

​Nan take matashin ya juyo ga Annabi Sulaiman (A.S) ya tambaya:

​“Wane ne wancan mutumin?”

“Kallon da yake yi mini k**ar bai taba ganin wani dan Adam ba kafin nan.

Ya kafa mini idanu sosai.”

​Annabi Sulaiman (A.S) ya amsa masa:

​“Wancan shi ne Mala'ikan Mutuwa.”

​Jin haka ya sa matashin ya kara kidima da tsorata kwarai da gaske.

Ya ce:

​“Ya Sulaiman! Dangane da yadda yake kallo na, na tabbata yana son ya karbi raina ne.

Don Allah ka taimake ni, ka yi mini wani abu.”

​Annabi Sulaiman (A.S) ya ce:

​“Mene ne kake so in yi maka?

Idan har lokacinka da aka dibar maka ya yi, me zan iya yi maka a kai?”

​Mutumin ya ce:

​“Ya Sulaiman, Allah ya ba ka ikon sarrafa iska.

Ka umarci iska ta kwashe ni ta tafi da ni mai nisa – zuwa kasar Indiya.”

​Ka yi tunanin irin wannan nisan!

Annabi Sulaiman (A.S) yana birnin Kudus (Jerusalem), yayin da kasar Indiya take da nisan dubban miliyoyi.

Sak**akon tausayawa, Annabi Sulaiman (A.S) ya amsa bukatar mutumin.

Ya umarci iska, kuma da izinin Allah, iska ta kwashe wannan mutumi ta lula da shi har zuwa kasar Indiya.

​A daidai lokacin da mutumin ya isa kasar Indiya, sai ya iske Mala'ikan Mutuwa yana jiran sa a tsaye.

Nan take Mala'ikan Mutuwa ya karbi ransa.

​TATTAUNAWA TSAKANIN ANNABI SULAIMAN DA MALA'IKAN MUTUWA

​Daga baya, lokacin da Mala'ikan Mutuwa ya dawo, Annabi Sulaiman (A.S) ya tambaye shi:

​“Me yasa ka rika zura wa wancan mutumin ido haka a cikin fadata?”

​Mala'ikan Mutuwa ya amsa da cewa:

​“Allah Ya umarce ni ne cewa in karbi ransa a kasar Indiya.”

“To sa'ar da na ganshi zaune kusa da kai a birnin Kudus, sai na cika da mamaki kwarai.

Na rika tambayar kaina yaya za a yi ya isa kasar Indiya alhalin Allah Ya kaddara cewa a can za a karbi ransa.”

“Amma sai gashi shi da kansa ya zabi ya yi tafiya zuwa kasar Indiya, kuma na same shi a daidai wurin da Allah Ya kaddara zan karbi ransa.”

​DARUSSAN DA KE CIKI

​Ya ku 'yan uwana maza da mata, Allah kadai Ya san a ina zamu mutu.

Allah kadai Ya san wuri, lokaci, da daidai sa'ar da hakan zata faru.

Kowane mutum an ba shi ajali tsararre a wannan duniya.

​Allah Madaukakin Sarki Yana cewa:

​“Kuma idan ajalinsu ya zo, ba su isa su jinkirta shi da sã'a guda ba, kuma ba su isa su gabatar da shi ba.” [Al-A'raf: 34]

​Lokacin da ajalinka ya yi, ba zai zo da wuri da sã'a guda ba, kuma ba zai makara ba da sã'a guda.

A daidai wannan lokacin, a daidai wannan wurin, Mala'ikan Mutuwa zai kasance a nan domin karbar ranka.

​Babu wanda ya isa ya tsere wa kaddara da tsarin Allah.

Kuna iya gudu daga wata kasa zuwa wata, kuna iya tsallake kasashe da teku, kuna iya boyewa a bayan katanga, dukiya, mulki, ko sarauta.

Amma lokacin da abin da Allah Ya rubuta ya zo, mutuwa zata same ku a daidai wurin da Allah Ya kaddara.

​Sak**akon haka, tambayar ba ita ce a ina zamu mutu ba.

Babban abin tambaya na gaskiya shi ne:

A wani hali zamu hadu da Allah?

​Shin zamu hadu da Shi ne muna masu yi Masa biyayya, muna ambatonsa, kuma muna shirin Lahira?

​Ko kuwa zamu hadu da Shi muna cikin shagala da dũniya mai shudewa?

​Kowace rai zata dandani mutuwa, kuma bayan mutuwa akwai haduwa da Allah (Subhanahu wa Ta’ala).

​Muna rokon Allah Ya kyautata karshenmu, Ya sanya kalmominmu na karshe su kasance “LA ILAHA ILLALLAH,” kuma ya sa mu hadu da shi alhalin Yana mai yarda da mu, Aameen.

~👨🏾‍💻✍🏾📝

05/06/2026

Ka yi nazari a kan waɗannan ayoyi na Alƙur'ani Mai girma.

﴿فَمَنْ أَبْصَرَ فَلِنَفْسِهِ﴾ [الأنعام: 104]
Duk wanda ya gane gaskiya kuma ya bi ta, amfanin hakan yana komawa gare shi ne.

﴿مَنْ عَمِلَ صَالِحًا فَلِنَفْسِهِ﴾ [فصلت: 46]
Duk wanda ya aikata aikin ƙwarai, to don amfanin kansa yake yi.

﴿وَمَنْ شَكَرَ فَإِنَّمَا يَشْكُرُ لِنَفْسِهِ﴾ [النمل: 40]
Duk wanda ya yi godiya, to amfanin godiyarsa yana komawa gare shi ne.

﴿وَمَنْ تَزَكَّىٰ فَإِنَّمَا يَتَزَكَّىٰ لِنَفْسِهِ﴾ [فاطر: 18]
Duk wanda ya tsarkake kansa, to ya tsarkake ta ne domin amfanin kansa.

﴿وَمَنْ جَاهَدَ فَإِنَّمَا يُجَاهِدُ لِنَفْسِهِ﴾ [العنكبوت: 6]
Duk wanda ya yi gwagwarmaya a tafarkin Allah, yana yi ne domin amfanin kansa.

﴿فَمَنِ اهْتَدَىٰ فَإِنَّمَا يَهْتَدِي لِنَفْسِهِ﴾
Duk wanda ya shiryu, to shiriyarsa tana amfanar kansa ne.

﴿وَمَنْ يَبْخَلْ فَإِنَّمَا يَبْخَلُ عَنْ نَفْسِهِ﴾ [محمد: 38]
Duk wanda ya yi rowa, to cutar rowar tana komawa gare shi ne.

﴿فَمَنْ نَكَثَ فَإِنَّمَا يَنْكُثُ عَلَىٰ نَفْسِهِ﴾ [الفتح: 10]
Duk wanda ya karya alƙawari, to laifin hakan yana kan kansa ne.

﴿وَمَنْ يَكْسِبْ إِثْمًا فَإِنَّمَا يَكْسِبُهُ عَلَىٰ نَفْسِهِ﴾ [النساء: 111]
Duk wanda ya aikata zunubi, to ya jawo wa kansa ne.

﴿قَدْ جَاءَكُمْ بَصَائِرُ مِنْ رَبِّكُمْ ۖ فَمَنْ أَبْصَرَ فَلِنَفْسِهِ ۖ وَمَنْ عَمِيَ فَعَلَيْهَا ۚ وَمَا أَنَا عَلَيْكُمْ بِحَفِيظٍ﴾ [الأنعام: 104]
Lalle hujjoji da shiriya sun zo muku daga Ubangijinku; wanda ya gane, amfanin hakan yana gare shi, wanda kuma ya makantar da kansa, cutar hakan tana kansa. Kuma ni (Annabi ﷺ) ba mai tsaron ku ba ne.

A waɗannan ayoyi, Allah Ya fayyace mana alhakin kowane mutum da sak**akon ayyukansa cikin bayani mafi ƙarfi da bayyana. Tsira a ranar Alƙiyama aiki ne na kai da kanka. Ba za a k**a ka da laifin gazawar mutane ba, sai dai za a tambaye ka game da irin sakacinka ga kanka.

Saboda haka, ka nemi taimakon Allah, ka dage, kada ka yi kasala. Ka ceci kanka.
Allah Ya datar da mu.

~👨🏾‍💻✍🏾📝

04/06/2026

I got over 30 reactions on one of my posts last week! Thanks everyone for your support! 🎉

04/06/2026

Ƙauna Shuka Ta Ake Yi

Ana shuka ta ne, sa'an nan a riƙa bin ta da ban-ruwa da kulawa har ta tsiro, ta girma, a girbi amfaninta. Ba a girbar abin da ba a shuka, kuma ba a tsirar da iri ba tare da wahalar reno ba.

Idan kana son a ƙaunace ka da gaske, to ka fara bayar da ƙauna. Ka zuba jarin lokacinka, ka nuna kulawarka, ka bayyana damuwarka da halin waɗanda ke kewaye da kai. Wanda yake tunanin zai girbi ƙauna ba tare da ya zuba hannun jarin kulawa da lokaci da tausayi ba, yana yaudarar kansa ne kawai. Misalinsa k**ar manomi ne da yake sa ran girbi alhali bai shuka iri ba.

Rannan na yi dogon rubutu kan sirri mai girma a cikin wannan ayar ta Alƙur’ani:

﴿وَأَنْ لَيْسَ لِلْإِنسَانِ إِلَّا مَا سَعَى﴾
“Kuma mutum ba shi da komai face abin
da ya yi ƙoƙari a kansa.”

(Suratun Najm: 39)

Wannan aya ba ta taƙaitu ga lahira kaɗai ba; ta shafi dukkanin al’amuran rayuwa. Rayuwa ma’auni ce ta abin da ka bayar, kafin abin da ka karɓa.

Idan kana son mutane su ƙaunace ka, to
ka kyautata musu da irin baiwar da Allah
Ya h**e maka. Idan kana da ilmi, ka ilmantar. Idan kana da kuɗi, ka taimaka ka warware matsala. Idan kana da matsayi ko alfarma, ka zama gada ta alheri. Domin zuciya tana karkata ne ga wanda ya amfanar da ita.

Hatta tsakanin iyaye da ƴaƴa ko ƴan'uwan juna, ƙauna tana ƙaruwa ne da kulawa, da ba da lokaci, da nuna damuwa. Ba a tilasta ƙauna; ana gina ta ne.

Amma wanda ya tsaya ƙiƙam tamkar gunki, yana jiran a so shi, ko yana jin wai dole ne a ƙaunace shi ba tare da ya bayar da komai ba, yana rayuwa cikin ruɗu ne. Kamar mai jiran kuɗi alhali bai nufi hanyar nema ba; ko mai jiran girbi alhali bai shuka ba.
Kuma wannan alama ce ta yadda ake gane butulu; duk wanda ba zai bayar ba, kuma yana jin ya cancanci ya ƙarba, to duk lokacin da masalaharsa ta ƙare a wajenka to zai juya maka baya.

Saboda haka, ka fara da shuka ƙauna. Ka bi ta da kulawa da bayar da lokaci. Sa'an nan ka ɗora da addu’a: Allah Ya tsare ka daga butulci. Domin akwai ciwo kyautatawa ga wanda ba ya godewa.

~👨🏾‍💻✍🏾📝

04/06/2026

KA DAINA BARIN AZABAR JIYA TA SACE MAKA NASARAR YAU, WANI LOKACIN TSAKANIN NASARA DA JARABAWA KARAMAR TAZARA CE!

‎Kowace rana da ka wayi gari ka gani, ba kawai wata rana ba ce da ta kara wucewa
a kalanda; wata sabuwar dama ce daga Allah domin ka sake tashi, ka gyara rayuwarka, ka kara kusantar burinka,
kuma ka zama mafi alheri fiye da jiya.

‎Sirrin Rayuwa: ‎
Kada ka bari raunin jiya ya hana ka ganin hasken nasarar da ke jiranka yau.

Abin da ya wuce ya zama tarihi; amma darasin da ka dauka daga ciki shi ne zai gina maka gobe.

‎Ka Tsarkake Zuciyarka: ‎
Ka daina ɗaukar nauyin abubuwan da
s**a riga s**a wuce.

Wanda bai iya sakin baya ba, ba zai iya rungumar gaba ba.

‎Ka Gina Kyakkyawan Tunani: ‎
Fara wannan ranar da kyakkyawan zato
da cikakken yakini.

Sau da yawa, irin tunanin da mutum
yake ginawa a zuciyarsa shi ne rayuwar
da yake gani a gaba.

‎Ka Dauki Mataki: ‎
Kada ka tsaya kana kallon nisan tafiya
har ka kasa motsi.

Babbar nasara tana farawa ne daga ƙaramin mataki guda ɗaya da aka dauka
da jarumtaka da juriya.

‎Ka tuna: ‎
Canjin rayuwa baya jiran sabuwar
shekara ko wata rana ta musamman.

Yana farawa ne daga wannan lokacin;
daga wannan safiyar; daga wannan shawarar da ka yanke a zuciyarka yau.



~👨🏾‍💻✍🏾📝

04/06/2026

Rayuwa babu aure ta fi wahala sama
da wahalar da ake tunani akwai a cikin
aure.

Rayuwa gabaɗaya cike take da wahal-
halu, kuma aure ko rashin aure duka
suna da nasu ƙalubalen. Sai dai aure
Sunnah ce ta Annabi ﷺ kuma hanya
ce da Allah Ya shar’anta wa mutane.
Annabi ﷺ ya kwaɗaitar da yin aure,
kuma ba zai umarci al’umma da abin
da wahalarsa ta fi amfaninsa ba.

Don haka, ya k**ata matasa su
rungumi aure da kyakkyawar niyya,
su shirya masa, su nemi taimakon
Allah, su yi haƙuri da ƙalubalen da
za su fuskanta. Haka nan, waɗanda
s**a gamu da jarabawa a aure ko
soyayya su yi dangana, su yawaita
addu’a, kuma su guji kushe aure ko
firgita mutane daga gare shi. Duk
wanda ya dogara ga Allah, Allah zai
sauƙaƙa masa al’amuransa kuma Ya
maye masa gurbin abin da ya rasa da
mafi alheri.

~👨🏾‍💻✍🏾📝

04/06/2026

Ƴan Arewa muna take gaskiya ne da gangan...

Mun san cewa a tsarin rayuwar mutane,
in dai ba ka daraja kanka ba, babu wanda zai daraja ka.

Mu kalli iya matsalar ƴaƴan da ake haifa
a watso kan t**i; babu abinci, babu ilmi, babu tarbiyya, yara ba su fi shekara 5
zuwa 7 ba, amma an bar su su ji da kansu.

Gwamnatoci da malamai da sarakuna da masu kuɗi da sauran manyan gari sun gagara warware wannan matsala tsawon shekaru, kullum ƙara haɓaka take yi.

Wannan bai isa abin kunya ba!

Ba mu san duniya tana kallon mu ba ne!

Yaya za a yi mutanen da ke irin wannan rayuwa su yi ƙima a idon sauran mutane?

In ba ka daraja kanka ba, babu mai daraja ka.

💔😞😡

~👨🏾‍💻✍🏾📝

04/06/2026

Mutumin kirki ba ya iya canja hali ya koma mugu, koda ya yi yunƙurin hakan ba ya nasara. Amma idan ƙalubalen rayuwa s**a yi masa yawa, ya ɗanɗana cutarwa da cin amana na mutane sosai, sai ya fara canzawa a hankali.

Zai canja daga mai yawan yafiya da uzuri da kawar da kai, ya koma wanda ba ya karɓar uzuri ko bayar da second change ga wanda ya cutar da shi.

Zai canja daga mai jajircewa wajen nuna soyayya da kulawa, ya koma wanda bai damu da kowa ba.

Zai canja daga tunanin ƙulla soyayya da abota da tunanin ɗorewar mu'amala har abada, ya koma wanda yake ganin kowa na zuwa ne na ɗan lokaci kuma zai tafi idan lokaci ya yi, ya daina sakin jiki da kowa, ya zama kullum a cikin shirin ko-ta-kwana na rabuwa yake.

Zai canja daga mai saurin yarda da mutane, ya koma mara yarda,wanda ke ɓoye sirrinsa da binne damuwarsa a zuciyarsa, da zaman kaɗaici, ya zama bai ɗauki komai na duniya da muhimmanci ba.

Zai daina ƙorafi, zai daina sa rai ga kowa, ko jiran kowa. Zai koma iya rayuwarsa ce kawai a gabansa. Akalar tunaninsa za ta canja, ya zama duk lokacin da ya ga mutane sharrinsu ne ke fara zuwa a ransa.

~👨🏾‍💻✍🏾📝

04/06/2026

Ban san abin da ke cikin gidajenku
ba, amma ina roƙon Allah Maɗaukaki:

Idan akwai mara lafiya a cikinsu,
Allah Ya ba shi lafiya cikin gaggawa;

Idan akwai mai cike da damuwa, Allah
Ya kawar masa da damuwar;

Idan akwai wanda ake bi bashi, Allah
Ya biya masa;

Idan akwai wanda ke cikin jarabawa,
Allah Ya yaye masa;

Idan akwai wanda ake yi wa hassada,
Allah Ya sa ya fi ƙarfin mahassadansa;

Idan akwai wanda aka yi wa sihiri, Allah
Ya karya shi.

Allah Ya ji ƙan magabatanmu da dukkan musulmai da s**a riga mu gidan gaskiya.

Allahumma Aameen. 🤲

Want your school to be the top-listed School/college in Kaduna?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Address

Kaduna