AMD Online News

AMD Online News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AMD Online News, Educational consultant, Bakin kasuwa Dogonjeji, Jama'are.

Har yanzu tuntuɓar masu ruwa da tsaki nake yi kan matakina na gaba a siyasa - Danjuma GojeTsohon gwamnan jihar Gombe, ku...
23/08/2026

Har yanzu tuntuɓar masu ruwa da tsaki nake yi kan matakina na gaba a siyasa - Danjuma Goje

Tsohon gwamnan jihar Gombe, kuma Sanatan da ke wakiltar Gombe ta tsakiya, Muhammad Danjuma Goje, ya ce har yanzu yana tuntubar mutane tare da yin shawarwari da masu ruwa da tsaki kan makomarsa ta siyasa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa shugabannin siyasa daga jam’iyyun PDP da ADC suna zawarcinsa tare da matsa masa lamba ya koma jam’iyyunsu, bayan da ya bayyana cewa jam’iyyar APC ba za ta ba shi tikitinta ba.

DA DUMI-DUMI: Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kafa Majalisar Yaƙin Neman Zaɓensa ta APC domin zaɓen 2027, inda aka naɗa tso...
22/08/2026

DA DUMI-DUMI: Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kafa Majalisar Yaƙin Neman Zaɓensa ta APC domin zaɓen 2027, inda aka naɗa tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, a matsayin Darakta-Janar (DG) na majalisar.

Fadar Shugaban Ƙasa ta sanar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa, Kashim Shettima, za su kasance Shugaba da Mataimakin Shugaban Majalisar Yaƙin Neman Zaɓen APC, yayin da Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, zai kasance Mataimakin Shugaban majalisar.

An kuma naɗa Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, a matsayin Sakatare na Majalisar Yaƙin Neman Zaɓen.

A ɓangaren jagorancin yaƙin neman zaɓen, an naɗa wasu manyan ‘yan jam’iyyar a matsayin Mataimakan Darakta-Janar, ciki har da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio; Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas; da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, waɗanda za su kula da harkokin yaƙin neman zaɓe a yankunan Kudu da Arewa.

Sanata Adams Oshiomhole zai kasance Mataimakin Darakta-Janar mai kula da tattara jama’a da gangamin siyasa, yayin da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa zai kasance Mataimakin Darakta-Janar mai kula da harkokin gudanarwa.

Haka kuma, James Abiodun Faleke, wanda ya taka muhimmiyar rawa a yaƙin neman zaɓen 2022/2023, zai dawo a matsayin Mataimakin Darakta-Janar mai kula da tsare-tsare, daidaita ayyuka da sa ido kan zaɓe.

Faleke zai yi aiki tare da daraktocin shiyyoyi guda shida, waɗanda s**a haɗa da Sanata Olushola Adeyeye a Kudu maso Yamma, Dr Ngozi Olejeme a Kudu maso Kudu, Sanata Uche Ekwunife a Kudu maso Gabas, Muntaqha Rabe a Arewa maso Yamma, Ahmed Muhammed Ketso a Arewa ta Tsakiya da Sanata Sani Danladi a Arewa maso Gabas.

A ɓangaren yaɗa manufofi da dabarun sadarwa, an naɗa Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris Malagi, a matsayin Daraktan daidaita harkokin kafafen yaɗa labarai da Strategic Communication.

Zai yi aiki tare da Dele Alake, Bayo Onanuga da Lanre Issa-Onilu, yayin da Tunde Rahman, Sunday Dare, Daniel Bwala da Felix Morka za su kasance Mataimakan Daraktocin daidaita ayyukan kafafen yaɗa labarai.

An kuma naɗa Segun Dada a matsayin Daraktan New Media, matsayinsa da ya riƙe a yaƙin neman zaɓen 2022, yayin da Solomon Arowolo zai kasance Sakatare na sashen New Media.

Majalisar ta kuma naɗa masu magana da yawun yaƙin neman zaɓen guda biyar, waɗanda Dele Alake ke jagoranta. Sauran sun haɗa da Alwan Hassan, Ayobami Oyalowo, Kemi Asekun-Sh*ttu da Adamu Fanda.

A cikin saƙonsa ga mambobin majalisar, Shugaba Tinubu ya buƙaci dukkan shugabannin sassan da aka kafa su yi aiki tuƙuru domin tabbatar da nasarar APC a zaɓen Janairu 2027.

Tinubu ya kuma buƙaci shugabannin sassan daban-daban su tuntubi sauran ‘yan jam’iyyar da ba a sanya sunayensu cikin jerin kwamitin ba, domin su ba su damar taka rawa a cikin yaƙin neman zaɓen.

Shugaban Ƙasar ya ce Gwamnatin APC ta cika alkawuran da ta ɗauka tare da sanya Najeriya a kan hanyar samun ci gaban tattalin arziki.

“Mun cika alkawuran da muka ɗauka a lokacin kamfen, kuma mun sanya ƙasarmu a kan hanyar samun ci gaban tattalin arziki. Tabbas mun fita daga duhun rami, kuma yanzu muna dab da girbar amfanin tattalin arzikin da zai amfani dukkan ‘yan Najeriya.”

Tinubu ya ƙara da cewa yayin da kamfen ɗin 2027 ke gabatowa, APC na da nasarori da dama da za ta gabatar wa jama’a.

“Yayin da muke shiga lokacin yaƙin neman zaɓe, muna da nasarori da dama da za mu bayyana. Mu nuna wa jama’a tarihin ayyukanmu da kwarin gwiwa, tare da ƙarfafa bege a kowane ɓangare na ƙasarmu.”

Ya kuma yi kira ga mambobin majalisar da su yi aiki domin kayar da duk wata ƙungiya da yake ganin tana son mayar da Najeriya baya.

Sanarwar ta fito ne daga Bayo Onanuga, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, a ranar 22 ga Agusta, 2026.

KBC Hausa

20/08/2026

Atiku Ya Bayyana Matakan da S**a Ɗauka Domin A Saki El-Rufa’i

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a baya, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa yana yin duk mai yiwuwa domin ganin an saki tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufa’i, daga tsarewar da yake fuskanta.

Atiku ya bayyana hakan ne yayin da aka tambaye shi kan ƙoƙarin da yake yi tare da wasu na ganin an saki El-Rufa’i.

"Muna yin duk abin da za mu iya domin ganin an saki El-Rufa’i. Muna ziyartarsa, muna aika masa da saƙonni, shi ma yana aika mana da saƙonni. Haka kuma, muna tallafa wa iyalansa,” inji Atiku.

AMD Online News

DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan Daba Sun Kai Wa Ayarin Gwamna Adeleke Hari a OsogboWasu da ake zargin ‘yan daba ne sun kai hari kan a...
19/08/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan Daba Sun Kai Wa Ayarin Gwamna Adeleke Hari a Osogbo

Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun kai hari kan ayarin motocin Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, a ranar Laraba, jim kaɗan bayan ya bar fadar Ataoja na Osogbo, Oba Jimoh Oyetunji.

Harin ya janyo musayar harbe-harbe tsakanin waɗanda ake zargin ‘yan daban da jami’an tsaron da ke rakiyar gwamnan.

An ce musayar harbe-harben ta ɗauki tsawon kimanin mintuna 12 zuwa 15, bayan Gwamna Adeleke ya bar zauren fadar sarkin, inda ya gana da masarautar.

Jam'iyyar APM mai alamar rogo ta lashe zaben dukkanin kananan hukumomin jihar BauchiJam'iyyar APM mai alamar rogo ta su ...
18/08/2026

Jam'iyyar APM mai alamar rogo ta lashe zaben dukkanin kananan hukumomin jihar Bauchi

Jam'iyyar APM mai alamar rogo ta su Gwamna Bala Mohammed ta lashe zaben dukkanin kananan hukumomin jihar Bauchi da aka gudanar.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar BASIEC ce ta ayyana hakan, yayin da take bayyana sakamakon zaben da aka yi a jiya Litinin.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Bauchi (BASIEC) ta sanar da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a faɗi...
17/08/2026

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Bauchi (BASIEC) ta sanar da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a faɗin jihar ranar Litinin, 17 ga Agusta, 2026.

A cewar hukumar, jam’iyyar APM ta lashe kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 20, yayin da ta kuma samu nasarar lashe 319 daga cikin kujerun kansiloli 323.

Ga sakamakon shugabannin ƙananan hukumomi:

Alkaleri: Bappah Aliyu Mohammed – APM, 107,482

Bauchi: Umar Mohammed Aliyu – APM, 125,170

Bogoro: Zakka Luka Magaji – APM, 25,282

Dambam: Iliya Isah – APM, 19,730

Darazo: Ya’u Samaila Sade – APM, 67,276

Dass: Mohammed Abubakar Jibo – APM, 35,264

Gamawa: Ali Babayo – APM, 54,423

Ganjuwa: Mohammed Idris M. – APM, 24,150

Giade: Mustapha Alhaji Musa – APM, 33,864

Itas/Gadau: Dankawuwa Ya’u – APM, 24,989

Jama’are: Inuwa Abdullahi – APM, 36,766

Katagum: Yusuf Babayo Zaki – APM, 65,626

Kirfi: Garba Musa – APM, 24,787

Misau: Salisu Hussaini – APM, 34,378

Ningi: Yahuza Adamu Haruna – APM, 29,387

Shira: Saleh Hodi Jibir – APM, 37,135

Tafawa Balewa: Sama’ila Wakili Lere – APM, 46,625

Toro: Abubakar Ibrahim Dembo – APM, 109,999

Warji: Habibu Idris Usman – APM, 43,066

Zaki: Mas’ud Aliyu – APM, 19,984

A bangaren kujerun kansiloli, SDP ta samu Dandango Ward a Bauchi, NRM ta lashe Darazo South Ward, ZLP ta samu Wandi Ward a Dass, yayin da YPP ta lashe Zirami Ward a Giade.

Shugabar BASIEC, Hajiya Jummai S. Abubakar (Gimbiyar Dass), ta ce hukumar ta tabbatar da sakamakon ne bayan kammala ƙirga ƙuri’u, tattarawa da tantance sakamakon, tare da bin tanadin dokar zaɓe.

Ta kuma taya waɗanda s**a yi nasara da al’ummar Jihar Bauchi murna.

Rahoto Zamani Tv

Sojoji na neman hana ni shiga Osun - Zargin mawaki DavidoFitaccen mawakin nan a  Nijeriya, David Adeleke, wanda aka fi s...
15/08/2026

Sojoji na neman hana ni shiga Osun - Zargin mawaki Davido

Fitaccen mawakin nan a Nijeriya, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya yi ikirarin cewa wasu sojoji na kokarin hana shi shiga Jihar Osun, yayin da ake gudanar da zaben gwamnan jihar a wannan Asabar.

Davido, wanda dan dan'uwan Gwamna mai ci Ademola Adeleke ne, ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X da aka tabbatar da sahihancinsa da sanyin safiyar Asabar, kamar yadda jaridar Punch ta rawaito.

Albashin Naira ₦70,000 ba za iya daidaita rayuwar ma'aikaci ba - NLCKungiyoyin ƙwadago a Nijeriya sun bukaci a gaggauta ...
07/08/2026

Albashin Naira ₦70,000 ba za iya daidaita rayuwar ma'aikaci ba - NLC

Kungiyoyin ƙwadago a Nijeriya sun bukaci a gaggauta sake duba mafi ƙarancin albashi a Nijeriya na ₦70,000, suna mai cewa ba zai isa ma'aikaci amfani ba a halin tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki.

05/08/2026

Madugun siyasar Dogonjeji District Kenan yana bayanin zaman sa daram a APC

Gwamnatin Osun ta garzaya kotu bayan EFCC ta rufe asusun kuɗin jiharBabban lauyan jihar Osun kuma kwamishinan shari'a, O...
05/08/2026

Gwamnatin Osun ta garzaya kotu bayan EFCC ta rufe asusun kuɗin jihar

Babban lauyan jihar Osun kuma kwamishinan shari'a, Oluwole Jimi-Bada, ya bayyana cewa gwamnan jihar ya ba shi umarni ya shigar da hukumar EFCC ƙara a kotu, bayan da ta daskarar da asusun gwamnatin jihar.

Jimi-Bada ya ce EFCC ta aika wa shugabannin First Bank, inda gwamnatin jihar ke ajiye asusunta, wata takarda mai umarnin "Post No Debit", wadda ke hana gudanar da duk wani cire kuɗi daga asusun, a ranar Laraba.

Ya ce wannan mataki na iya kawo cikas ga harkokin gudanar da gwamnatin jihar.

Address

Bakin Kasuwa Dogonjeji
Jama'are

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMD Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share