05/06/2026
Alhamdulillahi munyi sallar Juma'a lafiya, Allah ya karba mana dukka ibadun mu ya kuma sanya mu daga cikin bayin sa salihai.
Khalifan Shehu Manzo Gombe Na |||
05/06/2026
Alhamdulillahi munyi sallar Juma'a lafiya, Allah ya karba mana dukka ibadun mu ya kuma sanya mu daga cikin bayin sa salihai.
30/05/2026
Ziyara zawiyar Sheikh Ibrahim Ɓogo (RA)
30/05/2026
Ziyara raudar Maulanmu Shehu Manzo Gombe (RTA)
30/05/2026
A yanzu mun iso zawiyar Maulanmu Sheikh Ahmad Bolari (RA) domin gabatar da ta'aziyya da kuma gaisuwar sallah kamar yadda aka saba.
Allah ya jikan Alaramma Malam Mustapha Bolari.
30/05/2026
Alhamdulillahi mun ziyarci raudar Sheikh Modibbo Tukur RA.
Daga nan zamu zawiyar Sheikh Ahmad Bolari (RA)
30/05/2026
Ziyara zawiyar Sheikh Modibbo Jobbo (RTA)
Daga nan zamu nufi raudar Sheikh Modibbo Tukur (RA)
30/05/2026
A yanzu mun tashi daga zawiyar Maulanmu Shehu Manzo Gombe RTA domin fara ziyarori raudar daga cikin Shehunan mu na Dariqar Tijjaniyya a jahar Gombe.
Mun nufi raudar Sheikh Modibbo Jobbo dake bayan Gombe Division.
29/05/2026
Assalamu Alaikum..........
Muna sanar daku cewa, idan Allah ya kaimu gobe Asabar zamu gudanar da ziyarorin goron sallah kamar yanda muka saba a duk shekara.
Ga jerin wuraren da za'a ziyarya ɗaya bayan ɗaya
Raudar Sheikh Modibbo Jobbo
Raudar Sheikh Modibbo Tukur
Raudar Sheikh Ahmad Bolari
Raudar Shehu Adamu Manzo
Raudar Shehu Ɓogo
Za'a haɗu 09:00am za kuma a fara tafiya 10:00am
Da haka muke gayyatar dukka ahlin Tijjanawa dake cikin ƙwaryar garin Gombe daku halarci wannan ziyara mai albarka.
Allah ya kaimu ya bada ikon halarta. 👏
29/05/2026
Innā Lillāhi Wa Innā Ilaihi Rāji'ūn 😭
Cikin alhini da jimami muke sanar da rasuwar Alaramma Malam Mustapha Sheikh Ahmadu Bolari.
Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi masa rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa.
Za a gudanar da sallar jana'izarsa yau da ƙarfe 03:00 na yamma (3:00pm) a Zawiyar Maulanmu Sheikh Ahmadu Bolari (RTA).
Allah Ya jikansa da rahama, Ya sa mu cika da imani da kyakkyawan ƙarshe. Āmīn.
28/05/2026
⚠️ MUHIMMIN JAN HANKALI ⚠️
Mu a matsayinmu na Khalifofin Tijjaniyya, iyaye ne ga kowa, kuma ba mu da ɗan takara guda ɗaya tilo na raɗin kanmu. Tariqa ta fi ƙarfin a haɗata da siyasar wani ɓangare ko wata ƙungiya ta musamman.
Saboda haka, muna kira ga masoya da magoya baya da su guji danganta mu da siyasar wani mutum ko wata tafiya ta siyasa, domin hakan na iya haifar da rashin fahimta da kuma jawo mana baƙin jini a wurin wasu.
Kowa yana da ‘yancin ra’ayinsa na siyasa, amma idan mutum zai yi magana ko posting game da wani ɗan takara ko wata tafiya ta siyasa, to ya bayyana cewa:
"Wannan ra’ayina ne na kaina."
A matsayinmu na iyaye da shugabannin addini, akwai abubuwa da dama da suke haɗa mu da al’umma mabambanta, ciki har da ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban. Kuma ba sai siyasa kaɗai ba, domin akwai:
- gaisuwar murna,
- ziyara ta girmamawa,
- ta’aziyya,
- jajantawa,
- da sauran hakkokin zamantakewa da addini.
Saboda haka, ganinmu a wani waje ko tare da wani mutum ba yana nufin mun ɗauki matsayar siyasar duk abin da ake yi a wajen ba ne.
Muna kira ga al’umma da su kiyaye martabar malamai da shugabannin addini, tare da gujewa amfani da sunayenmu wajen tayar da saɓani ko rikicin siyasa.
Allah Ya tabbatar da haɗin kai, mutunta juna da zaman lafiya a tsakanin al’umma. 🤝