Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Aisha Muhammad, Aliyu Haidar
Ahlul Qur'an Hum Ahlullahi
We are highly appreciated if you happy we are a muslim
BAMBANCIN IZALA DA DARIKA 💥
Mece ce Darika Tijjaniyya; Darika kalma ce ta larabci dake ɗaukar ma'anar ( طَرِيقَة ) waton Ṭarīqah wani bin tsari ne ko muce hanya da mutum zai bi a kowane fanni na rayuwarsa ( Path ) Idan kaji ance Darika Tijjaniyya toh abinda ake nufi Hanyar tafarkin Tijjanawa.
Tijjani sunan wani Shehin malami ne ɗan kasar Algeriya shine ya kafa kungiyar Darika Tijjaniyya izuwa yanzu kusan shekaru ɗari biyu kenan 200 Years, Haka Darika Qadiriyya sunan shehin malami ne AbdulQadir Jilani Ɗan kasar Iraqi ne, Toh duk wannan kungiyoyi tana tafiya ne akan tsarin su da tafarkin su.
Mece ce ake nufi da Izalatil Bid'ah Wa Iqamatis Sunnah ; Kalmar ( إزالة ) waton Izālah kalma ce ta larabci tana nufin ( Gusarwa ) ko kace ( kawarwa ) Jam'in ma'anar itake ( Gusar da Bidi'ah Wa Iqamatis Sunnah da Tabbatar da Sunnah Manzon Allah Sallallahu alaihi 💞 ) wato kawar da duk wasu abubuwa da aka shigo dasu cikin addini ba tareda hujja daga Alkur’ani da Hadisi ba.
Wannan itake manufar kungiyar Izala a kawar da duk Bidi'o'i a k**a Sunnah Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, Darika Tijjaniyya kuma waton Hanyar Tijjani ko muce Hanyar AbdulQadir Jilani - Muna da tabbas akan Hanyar Manzon Allah itake kaɗai Hanyar tafarkin Allah domin Hujja acikin Alqur'ani Allah Ya tabbatar Manzon Allah shine Ɗan aike da ya turo ba Tijjani da AbdulQadir Jilani ba.
Allah Ubangiji Yasa Mu Dace 👏 💚 📊
Copied
Eid Mubarak
23/02/2024
Aduba Lamarin
22/02/2024
Alhamdulillah, Hajara Ibrahim Dan Axumi From Gombe State emerge 1st position at international musabaqa held at Jordan 🥰💗
ALLAH yaqarawa rayuwa Albarka YQarowa garimmu Gombe dakuma qasarmu ta Nigeria nasarori 🙏🙏
Karku Manta Daga Jihar Gombe take😀💗❣️🥰
Sa'an nan Malam Maimuna Hussaini Badaggi daga Kano tayi na (2) a Musabaqar da aka gabatar a kasar Iran
18/12/2023
SAQON GODIYA ZUWA GA PROF ISAH ALI IBRAHIM PHANTAMI
Assalamu Alaikum wa Rahmatullah.
A Madadin Ni Nura Abdullahi Bello Guiwa (MODIBBON SOKOTO) da Kuma Gwarzuwa *Aisha Abdulmutallib Yobe* Muna Mika Cikakkiyar Godiyar Mu ga *Professor Isa Ali pantami* akan Gagarumar Karramawa Da Yayi Mana da Kuma Kyautar Motoci da Yabamu Kirar *Corolla LE* biyo Bayan Samun Nasara Da Muka yi a Musabaqar qasa Shekarar da ta Shude. Allah ya Saka Masa da alkhairi ya biya da Gidan Aljanna.
Zanyi Amfani da wannan Dama inyi Kira ga Shuwagabannin mu akan Suyi Koyi da Professor Wurin qarfafa Duk Wanda Ya taka Wata Rawar Gani a Kowane Irin Fanni na karatun Addini Domin Zaburar Wa Ga Sauran Masu Tasowa.
Har Wa Yau Zanso in yi Kira da Jan Hankali ga Yan uwa da ake Cikin Gwagwarmaya Iri daya akan Cewa Wadannan Kyautuka Girman Su Bai Kai ace Niyyar Mu ta karkata Zuwa Yi Don Su ba. Asalin kyauta da Girmamawa Suna RANAR GOBE.
Allah yasa Muyi Saboda Shi Ya qara Mana albarka a Rayuwar Mu.
06/09/2023
Rayuwa kenan, shima gobe za'a sallace shi, wannan kadai ya ishemu wa'azi. Allah ya jikan Malam, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da imani.
06/09/2023
INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
إن الله ما أخذ وله ما أعطا وكل شء عنده لى أجل مسمى😭😭😭
A YAUNE MUKASAMI RASUWAN BABBAN MALAMIN MU WATO MALAM SHEIKH GIRO ARGUNGUN
WANDA KOWA YASANI MALAM YABAWA WANNAN ADDINI GUDUMAWA DA DUKIYARSA DA QARFINSA WAJEN GANIN WANNAN ADDINI YACIGABA BA DARE BA RANA BA SAFIYA BA YAMMA MUNYI BABBAN RASHI MUNA ROQON UBANGI ALLAH YAMASA RAHAMA YAQARFI KYAWAWAN AYYUKANSA YAKUMA YAFE MASA KUSA KURANSA.👏👏👏👏👏👏👏
05/09/2023
MALAM JA'AFAR BA DAN BOKO HARAM BANE
Wani Malamin bidi'ah boka mushriki ya fito yaci mutuncin Marigayi Malam Ja'afar ya kuma alakanta shi da Boko Haram, sai dai daga baya ya janye maganar bayan yaji za'a gurfanar dashi a Kotu
Abubuwan da zai sa mutum ya alakanta Malam Ja'afar da Boko Haram gasu k**ar haka:
(1) Kiyayya
(2) Banbancin akida
(3) Jahilci
(4) Wauta
(5) Dakikanci
Kiyayya: Idan kana kin mutum tabbas zaka iya masa sharri da kage idan har baka kasance mai adalci ba
Banbancin akida: Duk wanda zai budi bakinsa mai wari yace Malam Ja'afar dan Boko Haram ne idan ka duba zaka samu yana da banbancin akida da shi, akida na sa a wani lokuta a kasa yiwa juna adalci har ma ya kai ga sharri
Jahilci: Makiya Musulunci da suke da hannu a kafa Boko Haram sun ribaci jahilai matukar ribata, duk lokacin da jahili zai yi magana akan abinda bai sani ba to yana nunawa duniya jahilcinsa ne
Wauta: Wawaye su kan kafa hujja da maganar makiya ne ko abinda s**a ji a bakin wani ba tare da bincike ba, wauta kan sa mutum ya kasa fahimtar hakikanin gaskiya, domin har yanzu akwai wawayen da s**a kasa fahimtar makircin Boko Haram s**a koma yiwa su Malam Ja'afar sharri
Dakikanci: duk lokacin da dakiki zai yi magana da wahala kaga akwai ma'ana a cikinta, dakiki ne kawai zai dubi Malami irin Ja'afar yace masa dan boko haram, kiran Malam Ja'afar dan Boko Haram tsantsar dakikanci ne
Su kansu mayakan Boko Haram din da Shugabanninsu na farko da na karshe sun san Malam Ja'afar ba dan kungiyarsu bane, sun sha alwashin daukar rayuwarsa, kuma su s**a kashe shi bayan sun dawo daga Kasar Algeria koyon ayyukan ta'addanci tun kafin kaddamar da yaki a lokacin da suke gina akidar a cikin zukata
Mutane suna cikin duhun jahilci game da sha'anin Boko Haram da sirrinta da manufar kafata, har yau sun kasa fahimtar wadanda s**a tsara rikicin Boko Haram
Shiyasa yau ake samun wadanda suke zargin Malamai irinsu Malam Ja'afar da cewa sune s**a kafa Boko Haram saboda dakikanci da wauta
Ina tunawa, a wa'adin farko na Gwamnatin Buhari, an taba yin wani taro a jami'ar BUK inda aka gayyato Malamai da sauran kwararru a fannin tsaro aka tattauna mas'aloli akan Boko Haram da ayyukan ta'addanci domin a nunawa duniya tsantsar gaskiya akan Boko Haram
Irin wannan taro ne da ya k**ata ana gudanar dashi a kalla sau daya a duk shekara saboda fa'idarsa, amma tun da akayi sau daya ba'a sake yi ba
Muna da kundin bayanai na sirri da bincike da muka haddace a kwakwalwar mu akan Boko Haram, idan Allah Ya ja kwanan mu a duniya har Littafi akan tarihin Boko Haram da manufofinta sai mun fitar, a yanzu matsayin mu bai kai mu fitar ba saboda hatsarin dake tattare da hakan
Yaa Allah Ka karbi shahadar Malam Ja'afar da Albaniy Zaria
Allah Ka hadamu da su a cikin Aljannah Madaukakiya
26/05/2023
صباحل الخير
04/05/2023
INNALIL LAHI WA'INNA ILAIHIN RAJI'UN
Ana Cikiyar Wannar Baiwar Allah Mai Suna Aisha Yusuf Wanda Ta Bar Gida Zuwa Makaranta Gombe State University (GSU) Yau Kwana Uku Kenan Da Da Fitar Ta Kuma Wayanta Ankashe
Duk Wanda Allah Yasa Ya Ganta Ko Yaji Labarin Ta Ya Tuttubi Wannan Number
08083666637 Kokuma Ya Garzaya Da Ita Makaranta Gombe State University (GSU) Ko Police station
Allah Ya Bayya Nata Yasa Tana Halin Lafiya Amin
07/04/2023
Wannan shine Masallacin Usman Ibnu Affan a Gadon kaya
Wanda bayan dawowar Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam Aka Bude shi
A iya rayuwata Banga mutum irin Malam ba wajen Tawadhi'u da kokarin Da'awa da kokarin Fito da wasu bayin ALLAH da ba'a San baiwar da ALLAH ya zuba a kan su ba
Na samu zama da Malam gwargwadon Iko akalla karatun Wani littafin shk. Usaimin Kawaidil musla da Kitabuttauhid (Muhammad Bin Abdulwahb) siffatus salatun Nabiy (Albany),Riyadus salihin,Kashafus shubuhat, Ahkamul Jana'iz da Bulugul maram (Wanda in Prof. Sani Umar R/L ya dawo Hutu shi yake barwa ya ci gaba
Zama na da Sheikh ya bani Damar fahimtar sa a matsayin Mutumin da yake son masu ilimi yake Kuma kokarin hada ka da Duk Wani Mutumin kirki
A zaman da Nayi da sheikh na fahimci wasu Abubuwan da har Yau suna Yi min tasiri a rayuwa ta
1. Rashin tsoro: sheikh ya kasance Mai yadda da Duk hukuncin da ALLAH ya zartar masa a Wani lokaci da Ake gwagwarmayar naiman shari'a Wani cikin Yan uwa ya same ni kan cewar akwai wasu Daga cikin mutane Sun shirya don kawo cikas a Taron wa'azi da Aka shirya a masallacin Aliyyu bn Abu talib Wanda aka gayyato su IBB, Buhari da Abdussalam da nufin janyo su Don Saka su cikin harkar naiman shari'a
Sai su wadanchan Yan uwa s**a Yi wa Shirin mummunar fahimta inda s**a ce an siyar da gwagwarmayar shari'a ga su Gen. IBB Don harkar siyasa
A cikin masu waccan fahimtar Wani ya zagayo ya sanar Dani irin Shirin su na kawo cikas a Taron wa'azin da za'a gabatar
Bayan samun labarin na je Gadon kaya Don shaidawa Sheikh halin da Ake ciki Sheikh Bai dawo Gida ba har wajen 12 na Dare na Jira har ya dawo
Yana zuwa ya tarar da mutane na jiran sa yace Wanda mukayi alkawari s**a Jira ni su zan Gani
Wadanda ba muyi alkawari ba to suyi hakuri su dawo da azahar in ALLAH ya Kai mu
Haka Aka Yi bayan ya Gama ganin su ya kalle ni yace Gwagwarmaya Kai Kuma fa nace akwai Wani information da ya k**ata in sanar yace to zan shiga Gida in Tajdidin viser Sai in ji Daga wajen ka
Na Jira ya shiga Gida ba jima
Click here to claim your Sponsored Listing.