Ahmad Adamu Laja kashere

Ahmad Adamu Laja kashere Born in Kashere. Akko LGA, Gombe State

18/04/2026

Mu Tausayawa Marayu! 🥹

Sheikh Ja,afar Mahmoud Adam Rahimahullah

17/04/2026

ina taya murna Allah ya sa anbude a sa'a

ecwa church kashere

17/04/2026

TAMBAYOYI!
Wajabcin Hijabi Dakuma Matsayin Niqabi Ga Mace Acikin Shari,ar Musulunci !!!

Sheikh Ja,afar Mahmoud Adam Rahimahullah

05/04/2026

Yadda ake yin taimama a Musulunci

Sheikh Albani Zaria (rahimahullah)

Insha Allah daga kan Rarara an fara rushewa
05/04/2026

Insha Allah daga kan Rarara an fara rushewa

YAN KANIYA....Dubun dubatan Shedaniyawa ne suke gudanar da zanga zangar kin jinin yaki yau asabar a birnin Tel Aviv,suna...
04/04/2026

YAN KANIYA....

Dubun dubatan Shedaniyawa ne suke gudanar da zanga zangar kin jinin yaki yau asabar a birnin Tel Aviv,suna ta kiran shugabanninsu akan su dakatar da yakin da suke da Iran....

Yan kaniya aka ce basaji....

SANARWAR NAN TAKE4 GA AFRILU, 2026ADC TA SANAR DA KAFUWAR TSARIN WAKILAI NA MUSAMMAN A MANYAN BIRANEN DUNIYAJam’iyyar Af...
04/04/2026

SANARWAR NAN TAKE
4 GA AFRILU, 2026

ADC TA SANAR DA KAFUWAR TSARIN WAKILAI NA MUSAMMAN A MANYAN BIRANEN DUNIYA

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta sanar da kafa wani tsari na Wakilai na Musamman a manyan biranen ƙasashen waje, a matsayin wani sabon shiri na ƙarfafa hulɗarta da ƙasashen duniya da kuma inganta ɗaukar nauyin dimokuraɗiyya a Najeriya.

Wannan shiri ya zo ne sak**akon karuwar alamu na ayyukan da ba su dace da dimokuraɗiyya ba da kuma hare-haren da ake kai wa ‘yan adawa da shugabanninsu tun daga watan Yuli 2025, ciki har da yunƙurin rusa jam’iyyun adawa, raunana sahihin tsarin shugabancin jam’iyya, da kuma takaita shiga harkokin siyasa cikin ‘yanci.

A cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar a Abuja, ta ce wannan tsarin Wakilai na Musamman an kirkiro shi ne domin samar da tsayayyun hanyoyin sadarwa tsakanin ADC da manyan masu ruwa da tsaki na ƙasa da ƙasa, musamman a ƙasashe da cibiyoyi da ke ba da muhimmanci ga dimokuraɗiyya, haƙƙin ɗan Adam da kuma bin doka.

A karkashin wannan shiri, jam’iyyar za ta naɗa amintattun mutane a matsayin jakadu a wasu manyan biranen duniya da aka zaɓa bisa muhimmanci. Wadannan wakilai za su kasance manyan hanyoyin sadarwa tsakanin ADC da ƙasashen waje, majalisun dokoki, kafofin yaɗa labarai na duniya, cibiyoyin tallafawa dimokuraɗiyya, da kuma ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje.

Ta hanyar waɗannan hulɗoɗi, wakilan za su riƙa bayar da bayanai akai-akai kan muhimman batutuwa da s**a shafi yanayin siyasar Najeriya, ciki har da ci gaban siyasa, matsalolin haƙƙin ɗan Adam, tafiyar da mulki na dimokuraɗiyya, ingancin zaɓe, da kuma zarge-zargen danniya ga ‘yan adawa. Haka kuma za su isar da manufofin ADC da shawarwarin gyara ga masu ruwa da tsaki na duniya.

A cewar jam’iyyar, babban burin wannan shiri shi ne tabbatar da cewa abokan hulɗar ƙasa da ƙasa da cibiyoyin dimokuraɗiyya suna samun ingantattun bayanai masu gaskiya game da yanayin siyasar Najeriya, maimakon dogaro da bayanan gwamnati kaɗai.

ADC ta bayyana cewa ta hanyar kafa waɗannan hanyoyin hulɗa a hukumance, tana ƙarfafa amincinta a matsayin jam’iyya mai kishin dimokuraɗiyya, tare da ƙara tabbatar da kanta a matsayin madadin gwamnati mai inganci da ke da biyayya ga ka’idojin dimokuraɗiyya da kundin tsarin mulki.

Bisa la’akari da tasirin wadannan birane a duniya, jajircewarsu ga dimokuraɗiyya, da kuma yawan ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje, jam’iyyar ta zaɓi biranen Washington DC; London; Brussels; Berlin; Ottawa; Paris; Pretoria; Addis Ababa; Nairobi; Accra; Geneva; da New York a matsayin wuraren da za ta mai da hankali wajen hulɗar ta na ƙasa da ƙasa.

A wani ɓangare na wannan shiri, jam’iyyar za ta kuma kafa Tsarin tattara bayanai na ƙasa (National Documentation Initiative), domin tattarawa da rubuta duk wasu abubuwan da ke shafar shiga harkokin siyasa a fadin Najeriya. A karkashin wannan tsari, rassan jam’iyya na jihohi za su riƙa tattara bayanai kan abubuwa k**ar barazana, muzgunawa, hare-hare na tashin hankali, k**a ba bisa ka’ida ba, da kuma hana gudanar da ayyukan siyasa.

ADC ta jaddada cewa wannan shiri wani muhimmin mataki ne na ƙarfafa hulɗarta da ƙasashen duniya, inganta yaduwar sahihan bayanai kan siyasar Najeriya, da kuma ƙara nuna jajircewarta wajen kare dimokuraɗiyya, alhakin shugabanci, da haƙƙin ‘yan adawa.

An sanya hannu:

Malam Bolaji Abdullahi
Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa
African Democratic Congress (ADC)

‎💥BoomGWANA DISTRICT AGAIN‎‎Mutanen Gwana District suna cikin wani hali na damuwa da tashin hankali matuƙa‎‎Allah ya alb...
04/04/2026

‎💥Boom
GWANA DISTRICT AGAIN

‎Mutanen Gwana District suna cikin wani hali na damuwa da tashin hankali matuƙa

‎Allah ya albarkaci kasar Gwana da tarin arziki na noma da kuma ma'adanan ƙasa wanda hakan ya sanya wanzuwar arziki har zuwa makobtan yankin

‎Rashin zaman lafiya ya tilastawa mutanen Gwana district gudun hijira zuwa wasu garuruwan kusan wata biyu (2month) kenan

‎Bangaren gwamnati duk da ta turo Jami'an tsaro amma har yanzu ba aga kyakkyawar sauyi da ake zato ba

‎Muna ƙira ga gwamnati data duba ko ta sauya irin salon yakin ta da miyagu domin dawo da zaman lafiya mai dorewa a wannan yankin cikin ƙanƙanin lokaci

‎Ya zama wajibi gwamnati tayi dubi akan wannan yanki duba da irin tasirin ta wajen samar da abinci

‎A yanzu damuna muka dosa akwai buƙatar komawar su domin suyi noma

‎Gwana district guri ne da ake noma sosai wanda har mutanen jahohin makobta na zuwa domin noma

‎Abu na ƙarshe👇
‎Ya zama wajibi akan mutanen Gwana district su samarwa kansu hanyoyin samar da tsaron yankin su domin wallahi babu wanda zai samar muku da tsaron yankin ku sama da ku

‎(1) Zakuyi ƙungiyoyin tsaron gari wanda zai hada da matasa da kuma dottawa a kowani gari

‎(2) Zakuyiwa ƙungiyoyin rijista domin samun damar riƙe mak**ai

‎(3) Sannan ku sani babu daukar nauyi ko biyan membobin ƙungiyar domin bawai za'a mai dashi k**ar ƙungiyoyin ƴan baka bane

‎(4) Yazama wajibi ku hada kanku da sauran ƙungiyoyin tsaron kowani gari da kuma ƙauyuka saboda samar da haɗin kai tsaro mai ƙarfi

‎(5) Wajibi ne ku samar da Intelligent mutane daga cikin ku masu kawo muku bayanan sirri

‎Muna rokon Allah ya dawo muku da zaman lafiya mai dorewa mu kuma ya ƙara tsaremu da kariyar Sa

‎✍️Ahmad Adamu Laja








05/10/2025

Sheikh Alqasim Hotoro (Hafizahullah)

18/04/2025

Illa Da Hadarin Dake Cikin Zama Damasu Aikin Sa6o !!!

Sheikh Ja,afar Mahmoud Adam Rahimahullah

24/09/2022

Address

Gombe State

Telephone

+2348086468870

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ahmad Adamu Laja kashere posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The School

Send a message to Ahmad Adamu Laja kashere:

Shortcuts

Share