28/02/2026
Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya yi kira da a gabatar da gangamin Addu'o'i zuwa ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran, musamman Du'a'u Ahlu Thugoor.
_________
Akwai PDF na wannan addu'a, duba link a sashen sharhi don saukewa.
24/01/2026
“Har yanzu Sahibul Asr Waz Zaman (AS) ne ke tafiyar da abubuwa. Na sha fadin cewa, su fa Shi’a ba suna jiran Imam Mahdi (AS) ya zo ne su bi shi ba, su shi suke bi yanzu din nan ma. Kun san akwai masu tunanin Mahdi zai bayyana, in ya bayyana za a bi shi. To mu shi muke bi yanzu (haka). Kuma yana nan tare da mu, shi ke kwakkwafa al’amura.”
— Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky a ranar Nisfu Sha'aban 1443 (2022) a Abuja.
05/Sha'aban/1447
24/01/2026
18/01/2026
SABON LITTAFI MAI SUNA: TA'LIMATUL ISLAMIYYA: Koyarwar Addinin Musulunci.
Shiryawa da Bugawa: Makarantar Al-Kauthar, Makerar Gandu – Birnin Kebbi
Manufar Littafin
Littafin Ta’limatul Islamiyya an tsara shi ne daga zantukan Imam Khumaini (QS) domin tarbiyyar dalibai ta fuskar addini, domin ya zama hasken hanya mai sauƙaƙa fahimta ga yara da matasa a makarantu.
Yana koyar da muhimman abubuwan da kowane ɗalibi ya kamata ya sani game da addininsa, musamman ƴan gwagwarmayar musulunci.
Domin samun PDF na wannan littafin, ku ziyarci Telegram Chennel na Makarantar Al-Kauthar, ga link a comment section...
–Makarantar Al-Kauthar
12/01/2026
Ayatullahi Sayyid Ali khamene'i ya wallafa haka ne a shafinsa na X jim kaɗan bayan kammala gangamin nuna goyon baya ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran wadda al'ummar ƙasar s**a gudanar a yau 12 January 2026.
12/01/2026
UMMA ZEENATUDDEEN IBRAHEEM TA YI KIRA GA AL'UMMA DA MU KARANTA DU'AU AHLIS THUGUR GA JAMHURIYAR MUSULUNCI TA IRAN.
Karanta wannan addu'a ba iya Iran zai amfanar ba, hatta mu a nan Nijeriya zai amfanemu, musamman Ƴan Gwagwarmayar Musulunci.
Ga waɗanda ba za su iya karantawa ba; ku tura wannan sakon zuwa gaba, ku yi shere ga sauran al'umma, in kun yi haka kun sauke naku nauyi.
–Makarantar Al-Kauthar
11/01/2026
RAHOTO: SAƘON UMMA ZEENATUDDEEN IBRAHEEM GA ƳAN’UWA
A ranar Asabar, 10 ga watan Janairu, Malama Umma Zeenatuddeen Ibraheem (H) ta gabatar da muhimmin jawabi ga ƴan’uwa a Gwagwalada, wanda ya ta’allaka ne kan halin da al’ummar Musulmi ke ciki a wannan lokaci mai sarkakiya.
A cikin jawabin nata, Umma (H) ta ja hankalin ƴan’uwa sosai kan yawaita addu’a musamman ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran, wacce ke kan gaba wajen kare Musulunci, tsayawa kan gaskiya, da goyon bayan mazlumai a fadin duniya.
Daga cikin addu’o’in da ta fi jaddada a yi su a kullum akwai:
DU'A'U AHLIS THUGŪR
Wadda Imam Ali Zainul Abideen (A.S) ya koyar, ana karanta ta domin kariya ga Musulmi masu tsaron iyakoki da al’ummomi, da neman sauƙi ga raunanan duniya, da kuma rugujewar makiya da lalacewar makircin su.
Umma ta yi kira ga kowa ya ɗauki wannan addu’a da muhimmanci, musamman a irin wannan lokaci da tsarukan zalunci ke ƙoƙarin mamaye duniya.
Ga duk mai buƙatar PDF na wannan addu’a, za a iya samu ta hanyar ziyartar Telegram na Makarantar Al-Kauthar.
Link zai kasance a comment section.
– Makarantar Al-Kauthar
19/12/2025
An yi bikin karrama iyalan Shahidan Makarantar Al-Kauthar wanda s**a yi shahada a waqi'ar da ta auku shekarar 2004 a Birnin Kebbi, kimanin shekaru 21 da s**a gabata.
An gabatar da tarihi na abinda Sojojin Nijeriya su ka yi a wancan lokaci na yunkurin murƙushe tasirin Gwagwarmayar musulunci a Birnin Kebbi, amma basu yi nasara ba, dukda cewa sun zubar da jinin kimanin mutum biyar, tare da jikkata da dama daga ɗaliban Makarantar Al-Kauthar na wancan lokaci. Daga ƙarshe an gabatar da kyautukan girmamawa ga iyalan shahidai.
16/12/2025
🛡️ ADDU’AR KARIYA DAGA SHARRIN MAƘIYA
(An ruwaito daga Imam Ali alaihis salam)
📿 Wannan addu’a an ruwaito ta daga Imam Ali alaihis salam.
🕰️ Yadda ake karanta addu’ar
Imam Ali alaihis salam ya ce:
🌅 Ana karanta wannan addu’a kafin rana ta fito.
👉 Za ka karanta kafa ɗaya ka hura gabas 🌍
👉 Ka sake karantawa ka hura yamma 🌍
👉 Ka sake karantawa ka hura kudu 🌍
👉 Ka sake karantawa ka hura arewa 🌍
👉 Ka sake karantawa ka hura sama ⬆️
👉 Ka sake karantawa ka hura qasa ⬇️
👆 Sannan ka sake karantawa sau ɗaya, ka hura wa yatsanka,
🔄 sai ka zagaye kanka da wannan yatsan sau bakwai.
✨ Fa’idar addu’ar
⚔️ Duk abin da makiya za su yi, su yi.
🌍 Ko za su babbake duniya ne, babu abin da zai same ka.
🕊️ Kuma addinin Allah sai ya tabbata.
📢 Gargaɗi da ƙarfafawa
✅ Kowa ya tabbatar da ya yi aiki da wannan addu’a,
🛡️ domin addu’a ce makaminmu wanda ido baya gani.
💣 Ita ce Atomic Bom ɗinmu,
🗣️ kamar yadda Abba Sayyid Zakzaky (H) ya bayyana.
📌 Kowa ya tabbatar ya yi aiki da ita.
📤 Ku yaɗa domin sauran ƴan'uwa su amfana.
Makarantar Al-Kauthar
07/11/2025
FALALOLIN SALATI GA ANNABI DA IYALANSA ﷺ
(3) Daga cikin falalolinsa:
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Aalihi Wasallam) ya ce:
“Duk wanda ya yi salla, bai yi salati gareni da iyalaina a cikinta ba, ba za a karɓi wannan salla daga gare shi ba.”
📚 Kanzul Akhyar, shafi na 21
SALATI GA ANNABI DA IYALANSA — ginshiƙi ne na karɓuwar ibada, kuma alamar soyayya ga Manzon Rahma ﷺ da iyalansa tsarkaka.
🕌 Makarantar Al-Kauthar
05/11/2025
FALALOLIN SALATI GA ANNABI DA IYALANSA ﷺ
(2) Daga cikin falalolinsa:
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Aalihi Wasallam) ya ce:
“Salati gareni da iyalaina yana gusar da munafurci.”
📚 Kanzul Akhyar, shafi na 24
SALATI GA ANNABI DA IYALANSA — yana wanke zuciya daga riya, yana ƙarfafa imani, yana kuma kusantar da mu ga Annabi (S) da iyalansa tsarkaka.
🕌 Makarantar Al-Kauthar