05/12/2025
BANGAREN BOKO KAWAE
Assalāmu Alaikum,
Zuwa ga Maluma/ Iyaye/ Wakilan Dalibai,
Kamar yadda yake a jadawalinmu, an tsara dawowar makaranta a ranar Asabar, 6/12/2025.
Sai dai saboda umarnin rufe makarantun boko da gwamnatin jiha ta bayar, muna sanar da cewa an daga ranar komawa makaranta har zuwa lokacin da gwamnati za ta bayar da sabon umarni na bude makarantun baki ɗaya.
Lura: Wannan umarni ya shafi bangaren boko ne kawai. Bangaren Islamiyya kuwa, ana ci gaba da karatu kamar yadda aka saba.
Muna bai wa iyaye da wakilai hakuri bisa wannan sauyi da ya faru ba tare da tsammani ba, kuma muna godiya da goyon baya, fahimta da hadin kai da kuke ba mu a koda yaushe. 👏
Daga Hukumar Makaranta