Hamisu Nasidi Baban Auwaaab

Hamisu Nasidi Baban Auwaaab

Share

Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hamisu Nasidi Baban Auwaaab, Tutor/Teacher, Plot 2249 suite 8 zone 4 Plaza wuse zone 4 abuja, Abuja.

28/11/2023

Taba ka lashe!.

وما بكم من نعمة فمن الله.

Kada ka Raina duk wata kyauta da ALLAH ya baka. Ka

Rikeeta da kyau ka Godewa ALLAH in kayi sakaci ta kubuce maka zaka zubar da hawaye kafin ka kara samun kwatankwacinta.

Abinda ka rena watarana shi zai maka wahalar Samu.

19/11/2018

AN BAR GINI TUN RANAR ZANE...!

Nigeria wata kasa ce Mai Arziki da Yawan Jama'a. Kusan ba wata kasa da Dan Nigeria zaije yaji dadin zama a cikinta sama da Kasarsa.

Harkokin Nigeria kullum tabarbarewa suke, suna kara lalacewa, Al'umma tana dada shiga cikin Kunci da wahala, lamuran tsaro suna tabarbarewa, ayyukan ta'addanci suna kara yaduwa.

'Yan Nigeria 'yan tamore ne, ba abinda s**a sani sai kansu, kowa hankoransa shine ya zai gina kansa, ya rayu in yaso uban kowa ma ya mutu. Kai ko tukin mota kake a Nigeria zaka fahimci haka.

'Yan makaranta a Nigeria da zaka tambayesu meye burinsu? Zaka ji sunce Fatanmu mu kammala karatun nan Lafiya, mu samu aiki mai Gwabi. Ba wai su gina kasar ba.

Maluman Addinai a Nigeria wasu s**anyi s**a ga Nigeria ko suyi Babatu akanta ba dan komai ba sabida sun hango inda akayi Wawan Zama da Al'aurar kudin Nigeria zasu samu rabonsu.

Masu Mulki a Nigeria suna fafutukar kafa kansu ta karfin tsiya a mulki kawai dan su raunata Nigeria su kwashe arzikinta, su daukaka kansu ba ruwansu da Nigeria.

Gaskiya a Lamarin Gyaran Nigeria AN BAR GINI TUN RANAR ZANE..

Hanyar gyara a Nigeria shine a samar da wani tsari na dasa akidar Kasa da kishin kasa da muhimmancin kasa a zukatan Yan Nigeria.

11/10/2014

Aikin Mutanen Annabi Loud

Ubangiji Ta'ala ya misaltawa Quraishawa da labarin mutanen Garin SADUUM irin yanda ya halakar dasu a ayar dake cikin suratul Furqaan inda yace:-
وَلَقَدْ أَتَوْا عَلَى الْقَرْيَةِ الَّتِي أُمْطِرَتْ مَطَرَ السَّوْءِ أَفَلَمْ يَكُونُوا يَرَوْنَهَا بَلْ كَانُوا لَا يَرْجُونَ نُشُورًا
Wato su mushrikan larabawa sun kasance suna wucewa lokacin bulagoransu ta alkaryar mutanen Loud wadda aka halakarda duwatsu amman hakan besa sun dau izina ba, bari ma basa fatan kyakykyawan sakamako a yinin gobe kiyama.

Mutanen Annabi Loud sun kirkiri wata alfahsha (Namiji ya sadu da Namiji) babu wanda ya fara wannan danyen aikin kafinsu.
وَلُوطًا إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَتَأْتُونَ الْفَاحِشَةَ مَا سَبَقَكُم بِهَا مِنْ أَحَدٍ مِّنَ الْعَالَمِينَ
Malamai s**a ce in muka kalli alqur'ani da ido na Lura zamuga Allah ya anbaci Zina da Suna Alfahsha, ba tare da Alif da Laam ba.
وَلَا تَقْرَبُوا الزِّنَا إِنَّهُ كَانَ فَاحِشَةً وَسَاءَ سَبِيلًا
Amman da yazo kan aikin mutanen Annabi Loud se fade ta da Alif da Laaam
وَلُوطًا إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَتَأْتُونَ الْفَاحِشَةَ مَا سَبَقَكُم بِهَا مِنْ أَحَدٍ مِّنَ الْعَالَمِينَ
Sabida a nuna maka Munin abun kenan.

Malamai duk sunyi iittifaqi akan cewa da wanda yayi da wanda akayi da shi za'a kashe su ne gaba daya kamar yanda hadisi ya nuna.

Se dai yanda za'a zartar da hukuncin s**ayi sabani, cikin maganganu biyu.
wasu s**a ce
Za'a kona su ne da wuta
Wasu kuma s**ace za'a dora su a bene me tsaho a rufto da su.
Wannan duk yake Nuna munin aikin su, shi yasa da Allah ya halakar da mutanen Luud garin ma har yanzu ko Jirgin Sama baya wucewa yana nan a kasar Jordan inda ake kira da suna DEATH SEA.
Ya "yan uwa babu wani Annabi daga cikin Annabwa da Allah ya aiko da mugun aikin bayin sa ya cutar da Annabin irin Annabi Luud A.S
Domin malamai s**a ce zaka ga duk annabawa ana sanya sunan su a kowane zamani da lokaci kaji ansawa wani
Adam, Nuuh, Musa, Isah Harun Uzairu, Ya'aquub Ibrahim, Isma'il Ishaq ga Kuma sunan Abban Alkasim SAW.
Amman da wuya kaji wani da Suna Luudu ka kaji wani ance masa Abu luudu, sabida munin aikin su.
Kuskure ne a ringa kiran wannan mugun aiki da Suna Liwadi domin Allah da Annabi SAW ba su anbace shi da hakan ba.
Ko malamai in sun tashi magana akan aikin suna ce Masa Aikin mutanen Luud.
Allah ka karemu ka kare zuri'ar mu, masu yi Allah ka shirye su in ba masu shiryiwa bane ka kare musulmi na kwarai Sharrin su.
Hamisu Nasidi Baban Auwaab

26/ November/ 2013 A. D

11/10/2014

Addu'a....

Sau da yawa Allah ya kan jarrabi bawan sa nau'ika masu tarin yawa na jarrabobi a rayuwa.

Dalili guda biyune ya kansa Allah ya jarrabi bawansa. Ko dai an jarrabi mutum sabida yana da imani, hikmar hakan dan A bayyanawa duniya masu gaskiya cikin imanin su da kuma wadanda suke karya da da'awar imani a zukatan su.

Wani sa'in kuma Allah ya kan jarrabi bawan sa sabida wani kuskure da yake aikawatawa. Hikmar hakan dan ya tuba ya koma izuwa ga Allah ya kuma gyara kura-kuren sa gami da neman gafara me hade da nadama da kudirin baze kara zakkewa irin wannan kuskuren ba a abinda ya rage masa na rayuwar sa.

Duk lokacin da Allah ya jarrabi bawan sa da wani nau'i na musiba babba ko karama yana son abu 3 daga gareshi, wato hakuri da juriya gami da addu'a. Da wannan nake cewa:-

Allah mun tuba ka yafe mana, ka yaye mana damuwar da ke cikin zukatanmu, ka kuma cire mana kuncin rayuwar da muke ciki.

Mata da suke neman mazajen Aure Allah ya ka ba su mazaje na gari haka suma mazajen da suke neman aure ka basu mataye nagari wadanda suke da aure, allah ka wanzar da zaman lafiya a gidajensu, da kauna juna da wadata.

Allah iyaye ka taya su kula da tarbiyyar yaran su, ka tallage su cikin gajiyawar su, Allah ka shiryamu ka kimtsa mana zuri'ar mu cikin abinda kasi ka yarda dashi na zance ko na aiki.

Ya ubangiji ka sada mu da dukkan Alheri wanda muka sani da wanda ma bamu sani ba, Allah la karemu daga dukkan sharrin da muka sani da ma wanda bamu sani ba.

Ya Allah masu basuss**a akansa Allah ya yassare masu biyan bashin dake kan su, masu haya Allah ka h**e masu mahallinsu, masu cututtuka Allah ka basu lafiya, masu karatu Allah ka taimaka masu. Masu kasuwanci kasa masu albarka, ma'aikata ka albarkace su da kwazo da gaskiya da amana.

اللهم آجري المصآبّين في مصيبتهم وأخلفهم خيرًا منها....

اللهم آمييييييين

Baban Auwaab
11/october/2014 A. D
17/ zulhijjah/1435 A. H

Mobile uploads 08/10/2014

Hamisu Nasidi Baban Auwaab
4 mins ·
A kuya da Fatar Kare!!!

A kwanakin baya a kwai wasu "yan danfara da s**a addabi masu anfani da shafukan sadarwa na Facebook ta yanda suke turawa mutane sakon ayi magana da su ta hanyar Email da suke bayarwa ta haka ne, mutum ze magana da su ya sansu su sanshi.

Toh a yanzu akwai wata sabuwar hanyar yaudara da ta kara shigowa a Facebook inda zaka ana anfani da sunan mace musulma bahaushiya ana turowa mutane sako hade da number waya ana son su tura katin waya.

A iya zatona mace me tarbiyya ba zatayi haka ba. Amman ba mamaki bane dan anyi hakan duba da talaucin zuciya, da kuma tsatsar zuciya d nisantar mu da dokokin Allah.

Ga kuma yanda aka fahimci yanda mace take da tasiri a zukatan mazan da s**a kasa hakura su gamsu da matansu na aure, ko kuma samarin da dama yana daga cikin burin su na shiga Facebook shine samun alaqa da "yan mata. Wasu ma har alfahri suke da yawan "yan matan da suke mu'amala da su.

Muna yin Nasiha ga masu irin wannan dabi'a da suji tsoron Allah su dena su kyautata alaqarsu da Allah. Su nemi gafarar sa, su rokeshi cikin falalarsa su dogara da shi dogaro na hakika ta hanyar tashi su nemi na kansu.

In kuma mata ne suke wanann dabi'ar suji tsoron Allah su rike kimarsu da mutuncin su da kuma dabi'ar da aka san mace dashi na kunya da kamun kai.

Larabawa suna cewa:-

تجوع الحرة ولا تأكل بثدييها....

Allah ka tsarkake mana zukatanmu, ka kula mana da tarbiyyar Al'ummar mu, ya Allah ka h**e mana wadatar zuciya.

Hamisu Nasidi Baban Auwaab
15/Zul-Hijjah/1435 A. H

06/10/2014

A kula.....

"Yan Uwa akwai wani Shafi a Facebook Me suna Sahara Reporters, basu da aiki sai zagin addinin musukunci da cin mutuncin musulmai da alqur'ani me girma.

In muka kula da kyau ya banbantada Sahara Reportersda ya saba kawo labarai da rahotanni wanda galibinsu na siyasa ne kuma babu bangarencin addini ko yare a cikin sa.

shi wannan shafi kacokan in kuka duba shi zaku ga kamar yana son haddasa rigima ne a tsakanin al'umma masu mabanbantan addinai a Nigeria. Dan haka muke kira ga Company Sahara Reporters na Jarida su fito suyi mana bayani shin shafin su ne ko kuwa wasu nne suke anfani da sunan su? in na sune suji tsoron Allah su kare mana martabar addinin mu. in ba haka ba muna gaya masu musulmai ba ragwage bane akan addinin su.

in kuma bana su bane suyi mana bayanin da zamu gamsu kuma su dauki matakin da ya dace wajen nesanta kansu da wancen shafi da yake cin mutuncin addinin mu.

muan kira ga hukuma tasa ido akan shige da ficen mutane a yanar gizo dan tabbatar da tsaro da zaman lafiya a tsakanin al'umma. kasashe da dama sun sami matsala kasar su ta hargitse sabida saka i da rashin kula da al'amuran da s**a shafi sadarsa ta gama gari wato social networks.

muna kira ga masana dake cikin musulmi us dage da rubutu akan wance shafi da nuna hadarin dake tattare da shi, bar a jawo hankalin mahunta akan wannan matsala.

allaha ka bawa addininmu kariya.

Hamisu Nasidi Baban Auwaab
11/Zul-Hijjah/1435 A. H

04/10/2014

Sallar Idin Layya:
1. Jama'a ina mana barka da salla. Allah ya karbi ayyukanmu na kwarai, ya yafe mana kurakuren mu, ya sanya mu cikin 'yantattun bayinsa. Ameen.
2. Musulmi suna da idi guda biyu da Allah ya zaba musu, a madadin na jahiliyya, su ne Idul Fitr, da Idul Adh'ha. (Muslim #1218).
3. Fita zuwa sallar idi farilla ce, bisa magana ta malamai mafi inganci. (Bukhari #342, Muslim #890).
4. Kuma ana yinta ne bayan rana ta d**o har zuwa zawali, bisa ijma'in malamai.
5. Yana da kyau a yi sammakon yinta, musamman sallar layya, domin mutane su samu damar cin naman layyarsu da wuri. (Bukhari #951). Sabanin idul fitr, ana son jinkirta kadan saboda mutane su samu damar fitar da zakkar fidda-kai.
6. Sunnar Annabi (S.A.W) ita ce yin sallar idi a Filin idi, ba a cikin masallaci ba. (Bukhari #956, Muslim #889). Sai dai idan akwai uzuri kamar ruwan sama to babu laifi a yi ta a masallaci.
7. Yawancin malamai suna ganin cewa, mutanen makka ya fi musu, su yi ta a cikin masallacin Harami, domin akan haka aikin malamai magabata ya gudana.
8. Yana da kyau mutum kafin ya fita idi ya yi wanka ya sanya ti**re, kamar yadda ya tabbata daga aikin Ali da Abdullahi ibn Umar (RA).
9. Mutum ya yi ado da sababbin kayayyaki masu kyau. (Bukhari #948, Muslim #2068). Wannan hukuncin ya shafi maza ne kadai banda mata (Abu Dawud #565, Ahmad #6118).
10. Yana da kyau ya fita yana kabbara. (Baqarah, Aya:185).
11. Kuma ana fita har da 'yammata da tsofaffi da masu al'ada, sai dai masu al'ada za su nisanci wurin sallah. (Bukhari #971, Muslim #890).
12. Sunna ce mutum ya sa6a hanya wajen tafiya da komawa gida idan hakan zai yiwu. (Bukhari #986).
13. Sallar Idi ba ta da nafila a gabaninta ko a bayanta. Sai dai mutumen da ya saba sallatar walaha zi iya sallatarta kafin idi. (Bukhari #989).
14. Liman zai musu salla ba tare da kiran salla ko ikama ba. (Bukhari #960, 961, Muslim #885, 886).
15. Sallar idi raka'o'i biyu ne kacal, bisa ijma'in malamai. (Ahmad #257 Nasa'i #1420, Ibn Majah #1063).
16. A raka'ar farko zai yi kabbara (7) bayan kabbarar harama. A raka'a ta biyu zai yi kabbara (5) bayan kabbarar tsayuwa. (Abu Dawud #1149-1150, Ibn Majah #1280).
17. Kabarbarin nan mustahabbi ne ba wajibi ba, don haka barinsu bisa kuskure ko dagangan ba ya bata salla.. Wannan babu sa6ani akansa a gurin malamai.
18. Babu wani abu da ya zo daga Annabi (S.A.W.) na zikiri tsakanin wadannan kabarbari. Sai dai an samu daga wasu daga cikin sahabbai irin su Ibn Mas'ud, da Abu Musa, da Huzaifa, suna cewa, bayan duk wata kabbara zai yi hamdalah da salati ga Annabi (S.A.W). Wannan shi ne ra'ayin Imam As-Shafi'i, da Ibn Taimiyya. (Baihaqi 3/291).
19. In ya ga dama ya daga hannu tare da kowace kabbara, kamar yadda Ibn Umar yake yi a kabarbarin sallar janaza. In ya so kuma ya bari, saboda rashin tabbatar wani hadisi daga Annabi (S.A.W.) akan hakan. (Al-Mughni 2/120).
20. Mustahabbi ne ya karanta fatiha da suratul A'la a raka'a ta farko, ya karanta suratul Ghashiyat a raka'a ta biyu. (Muslim #878). Ko ya karanta Suratu Q, a raka'a ta farko, da suratul Qamar a raka'a ta biyu. (Muslim #891).
21. Sannan liman ya yi huduba bayan salla. Wannan ijma'i ne na malamai. (Bukhari #961, 962 Muslim #885, 884).
22. Sauraren wannan hudubar mustahabbi ne ba wajibi ba, bisa ijma'in malamai. (Abu Dawud #1155, Nasa'i #1571, Ibn Majah #1290, Al-irwa' #629).
23. An shar'anta yin kabarbari a ranekun idi a ko ina ba wai sai bayan sallolin farilla ba kadai. Babu wani hadisin Annabi (S.A.W) da ya inganta akan hakan. Amma akwai aikin wasu daga cikin sahabbai kamar Ali, Ibn Abbas, Ibn Mas'ud (Allah ya yarda da su), kuma akan hakan ne aikin musulmi ya gudana.
24. Babu wata sigar kabbara ta musamman da ta zo daga Annabi (S.A.W). Amma an samu daga wasu sahabbai kamar Ibn Mas'ud Ibn Abbas da Salman Al-Farisi (Allah ya yarda da su).
25. Yana da kyau musulmi su rika yiwa junansu murnar barka da salla. Kamar yadda aka samu sahabbai suna yiwa junansu, har suna cewa, "Taqabbalallahu Minna wa minka". (Fathul Bari 2/446, Tamamul Minnah, shafi #354).
Allah ya karba mana, ya maimaita mana. Amin.

Daga shafin Dr. Muhd Sani Umar R/lemo... Hafizahullah

03/10/2014

Taba ka Lashi....

Ranar Arfah, Ranar farin ciki Al'umma...... Ranar bakin cikin Shaidan......

Shaidan be taba ganin wata ranar kaskanci da wulakanci da bakin ciki a gare shi ba, fiye da ranar Arafah.

Domin irin yanda yake ganin Allah yana saukar da rahmarsa, yana kankare manyan zunubai ga bayin sa.

Duba Muwadda ta ImAm Malik daga Hadisin Abud-Dar-daA'i Allah ya kara masa yarda.

Yi kokari kayi abinda Allah ze gafarta maka a wannan rana dan ka bakanta ran makiyin ka shaidhaan!!!

Hamisu Nasidi Baban Auwaab
9/zul-hijjah/1435 A. H

01/10/2014

Taba Ka lashe!!!!

Mutanen kirki Allah ne yake son su yake tsarkake su, yake kuma basu kariya daga dukkan kaskanci har ma da sabo!!!

Duk wanda Allah yayiwa Baiwar Salaha zaka ga ba ruwan sa da abubuwa na shirme, in ance yayi ma kunyar mutane yake ji, baya ga tsoron Allah da ya mamaye zuciyarsa.

Inda Allah ze jarrabi wani mutumin kirki daya da aikata abinda be dace ba, se kaji duniya tayi caaaaa akansa ana ta tofa albarkacin baki akan wannan kuskure daya da ya aikata, har ma wani sa'in a manta da dukkan alkhairansa.

Amman in kaga mutum yana sheke ayar sa, ba wanda ya damu dashi kada ya dauka hakan alkhairi ne a gareshi, alkhairi shine kayi kuskure Allah ya baka ikon gyara tun kana da rai da kuruciyar ka.

Abin Allah ya kiyaye Yau inda wani Malamin Sunnah a kano ze yi wa'azi ya duura ashar, nayi Imani bama shi da yayi ashariyar ba lefin se ya mamaye dukkan malaman sunnah, dake kano da kewaye... Ana ta cece kuce!! Sabida yanda Allah yake nufatar su da Alheri. Amman Ga عَبْدٌُ ُ جَبَّار ya dura ashariyar da ko yaro karami in yana da tarbiya ba ze yi taba. In kuwa yayi magabata s**a ji zasu kwabe shi.

Ina maka Nasiha Sabida Allah ka tuna cewa shi Ilimi amana ce dole ka kare shi yanda Allah da annabi SWA s**a koyar.

Daukakar Da Malam Naka ya samu har kakai matsayin da kake kai, be same ta hanyar duura ashariya ba.

Kana da sauran Lokacin Tuba da samarwa kanka nutsuwa, tun kafin damar da kake da ita tafi karfin ka. Dan nayi Imani Allah yana maka kiwon ragon Layya ne.

ولو يعلم الكبش أن القائمين علي .....

تسمينه يضمرون الشر ما أكلا

Yaran da kake ganin suna maka ihu kana zaton daukaka ce, a zahiri kabi a hankali kada ta zame maka Daukakar biri yana kara tsalle yana sama ana ganin al'aurarsa, masu ihu suna Alalo Alalo Tabakaka!

Kurarin da kake kasan kururuwar jajibire ce, ba zata taba bawa Alfadari tsoro ba, dan yasan baya cikin dabbar yanka.

Jiyar ka bata rage komai ba, b***e yau dinka
Allah yana cewa:-

أَنزَلَ مِنَ السَّمَاءِ مَاءً فَسَالَتْ أَوْدِيَةٌ بِقَدَرِهَا فَاحْتَمَلَ السَّيْلُ زَبَدًا رَّابِيًا وَمِمَّا يُوقِدُونَ عَلَيْهِ فِي النَّارِ ابْتِغَاءَ حِلْيَةٍ أَوْ مَتَاعٍ زَبَدٌ مِّثْلُهُ كَذَٰلِكَ يَضْرِبُ اللَّهُ الْحَقَّ وَالْبَاطِلَ فَأَمَّا الزَّبَدُ فَيَذْهَبُ جُفَاءً وَأَمَّا مَا يَنفَعُ النَّاسَ فَيَمْكُثُ فِي الْأَرْضِ كَذَٰلِكَ يَضْرِبُ اللَّهُ
الْأَمْثَالَ

Har kullum addu'ar da Sheikh Umar Sani fagge yakeyi tana min tasiri kuma tana burgeni ina yawan yinta .

اللهم يا ربنا إذا أعطيتنا مالاً أو علمًا أو منسباً فلا تأخذ سعادتنا.....

Hamisu Nasidi Baban Auwaab
1/zul-hijjah/1435 A. H
25/09/2014 A. D

Want your school to be the top-listed School/college in Abuja?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Category

Telephone

Website

Address

Plot 2249 Suite 8 Zone 4 Plaza Wuse Zone 4 Abuja
Abuja