02/04/2025
DUNIYA TSOHON GARI
Sadiq Tukur Gwarzo
Alkur’ani mai tsarki ya bayar da labarin mutanen ‘Ād (Adawa), wata tsohuwar al’umma da ta kasance mafi ƙarfi da ɗaukaka wadda ba a taɓa ganin irinta ba a duniya.
Labarinsu ya ja hankalin malamai, masana tarihi, da masu binciken ƙasa tsawon ƙarnoni. An siffanta su a matsayin al'umma masu girman jiki da s**a ƙi bin umarnin Allah, daga ƙarshe Allah ya shafe su daga tarihi, abin da ya sa labarinsu ya kasance darasi ga sauran al'umma.
A cikin ayoyi da dama, Alkur’ani ya bayyana ƙarfinsu. Allah ya aiko Annabi Hūd (A.S) don ya shiryar da su, amma s**a ƙi karɓar saƙonsa, s**a yi girman kai, sannan s**a ci gaba da zalunci da almubazzaranci.
Allah ya siffanta su da cewa ba a taɓa yin irinsu ba:
"Shin, ba ka gani yadda Ubangijinka Ya yi wa ‘Ād—[na] Iram, birnin da ke da manyan ginshiƙai, wanda ba a taɓa yin irinsa ba a duniya?" (Alkur’ani 89:6-8)
Malamai irin su Ibn Kathir sun bayyana cewa ‘Ādawa mutane ne masu tsayi da ƙarfi, kuma sun ƙware wajen gine-gine. Wasu ruwayoyi sun ce suna da tsayi har zuwa kimanin ƙafa 90 (ninkin tsawon mutanen yanzu sau 15). An ce sun gina manyan gine-gine masu haske da ƙawa da ababen alatu, wanda birninsu Iram ya ƙunshi tsararrun ginshiƙai da hasumiyoyi masu girma.
Malamai da dama sun bayyana girma da kuma halakar da ta faru ga ‘Ādawa.
Ibn Kathir, a cikin littafinsa Qasas al-Anbiya, ya bayyana cewa mutane ne da s**a fi sauran al’ummomi ƙarfi kuma sun gina manyan birane. Ya kawo ruwayoyi da ke cewa tsayinsu ya kai har cubit sittin (kimanin ƙafa 90). Amma saboda girman kai da rashin godiya, Allah ya aiko musu da wata iska mai azaba har tsawon darare bakwai da kwanaki takwas har sai da s**a rushe (Alkur’ani 69:6-7).
Imam Al-Tabari, a cikin tafsirinsa, ya bayyana cewa mutanen ‘Ādawa sun kware a gine-gine kuma sun gina manyan gine-gine da s**a fi kowane zamani girma. Ya kuma ambato ruwayoyi da ke nuna cewa an binne ragowar gine-ginensu a cikin hamadar Larabawa.
Gaskiyar Kimiyya da Binciken Tarihi
A cikin shekarar 1992, masana tarihi sun yi amfani da hotunan tauraron dan adam da tsoffin taswirori domin gano wani birni a cikin hamadar Rub' al Khali a Oman, wanda ake kira Ubar, ko kuma Iram Mai Ginshiƙai. Bincike ya nuna cewa birni ne da ya bunƙasa a cinikayya kafin ambaliyar yashi ta binne shi.
A cikin watan Maris na shekarar 2025 ne masu bincike Corrado Malanga na Jamiar Pisa, ta ƙasar Italy da Filippo Biondi na jamiar Strathclyde ta ƙasar Scotland, da sauransu s**a fitar da rahoton binciken wasu manyan hasumiyoyi da hasken SAR ya hango a ƙarƙashin dalar Giza na ƙasar Misira wanda kan iya sauya ɗaukacin tarihin da aka jima ana bayarwa game da Misira, a cewarsu tsayin hasumiyoyin guda takwas sun kai kimainin ƙafa 600, kuma sune ke ɗauke da dalar duwatsun Giza, abinda ya sanya mamaki a zukatan mutane musamman game da yadda mutanen da s**a rayu kimanin shekaru dubu uku zasu mallaki fasahar aiwatar da waɗannan gine-gine.
A zance mafi inganci, daga al'ummar Adawa da ake hasashen sun rayu a inda ƙasar Oman take a halin yanzu, zamu iya fahimtar cewa mutanen da s**a rayu gabanninmu sun mallaki fasahohin gine-gine da ƙere-ƙere waɗanda har yanzu ba a kai ga riskar kwatan-kwacinsu ba, sannan da yawansu sunyi fito na fito da Allah, don haka Allah ya halakar dasu tare da shafe tarihinsu a bayan ƙasa.
Tabbas, babu wani ƙarfi daya kusanci ƙarfin Allah. Kuma dukkan mai rai mamaci ne, amma Allah Ta'ala rayayye ne kuma wanzajje.
22/02/2025
08/10/2024
04/09/2024
20/08/2024